Majalisar jihar Kaduna za ta ɗauki mataki kan yaron El-Rufa’i

0
54

Daga Idris Umar, Zariya

Tuni Majalisar ta bayyana cewa, majalisar jihar Kaduna za ta ɗauki mataki kan Bello El rufa’i kan barazanar da ya yi wa Shugaban Majalisar jihar a WhatsApp.

wata sanarwa da Majalisar jihar Kaduna ta fitar Mai ɗauke da sa hannun Malam Suraj Bamalli Mataimakin kakakin Majalisar ta Jihar Kaduna yana cewa dangane da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, Majalisar dokokin jihar Kaduna na ƙoƙarin ganin ta magance munanan kalaman da Hon. Bello Elrufai, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Kaduna ta Arewa.

Jim kaɗan bayan kafa kwamitin da zai binciki harkokin kuɗi, rance, tallafi, da aiwatar da ayyuka daga 2015-2023 a jihar Kaduna, Hon. Bello Elrufai ya shiga kafafen sada zumunta da rubutu guda biyu, yanzu kuma an goge shi, inda ya yi ƙira da a zo ayi rigima da kuma rashin mutunta ɗaukacin ɓangaren majalisar da gwamnati. Bugu da ƙari, ya aike da saƙonnin ɓatanci da zagon ƙasa ga Kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman ta WhatsApp.

KU KUMA KARANTA: Majalisar dokokin jihar Kaduna za ta fara binciken El-Rufai

An yi ta yaɗa hotunan waɗannan saƙonni da saƙonnin twitter, lamarin da ya jawo damuwa a tsakanin al’ummar jihar Kaduna. Abin takaici ne yadda ɗan Majalisar Tarayya da aka ba wa al’ummarsa amanar wakilcin al’umma zai yi irin wannan ɗabi’a, yana ƙoƙarin kawo cikas ga ayyukan Majalisar Jiha.

Majalisar dokokin jihar Kaduna tana son tabbatar wa al’ummar jihar Kaduna nagari cewa ta tsaya tsayin daka wajen yin hidima ba tare da tsoro ko son rai ba. Mambobin Majalisar sun yi rantsuwar tabbatar da ingancin ofishinsu da kuma tabbatar da cewa sun taka rawar gani wajen gudanar da ayyukansu, ba tare da la’akari da wani yunƙuri na tsoratarwa ko barazana ba.

Barazana da tsoratarwa daga kowa, ciki har da ‘yan majalisar tarayya ba za su hana majalisar dokokin jihar Kaduna yin adalci da riƙon sakainar kashi ba. Majalisar dai ta tsaya tsayin daka wajen ganin ta samar da daidaito da kuma tabbatar da doka a jihar Kaduna.

Muna ƙira ga al’ummar jihar Kaduna nagari da su kasance masu lura da tsayin daka wajen ganin an tabbatar da gaskiya da riƙon amana da bin doka da oda. Majalisar dokokin jihar Kaduna za ta ci gaba da biyan bukatun jihar da al’ummarta.

Leave a Reply