Connect with us

Al'ajabi

Zulum ya bada sanarwar tallafin naira biliyan ɗaya ga waɗanda gobarar kasuwa ta shafa a Maiduguri

Published

on

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya sanar da bayar da agajin gaggawa na naira biliyan 1 ga waɗanda gobarar kasuwar Monday Market ta shafa a Maiduguri, jihar Borno.

Gwamnan ya ziyarci kasuwar da safiyar lahadi bayan da gobara ta ƙona kantuna da dama. Ya ce kuɗaɗen za su bayar da tallafin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa, har sai an tantance lamarin.

Mai magana da yawun gwamnan, Malam Isa Gusau, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce Zulum ya ziyarci wurin da lamarin ya faru, ya kuma haɗa da sojoji masu ɗauke da makamai domin tabbatar da tsaro a yankin domin daƙile taɓarɓarewar doka da oda.

Sanarwar ta ce, “Mun tashi ne a yau da wani mummunan bala’in tashin gobara a kasuwar litinin da ke Maiduguri. Wannan abin takaici ne matuka, amma mun yi imani da cewa Allah ne ya kaddara. Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun. Na ji zafi sosai da wannan lamarin kuma na san yadda yake da zafi ga kowa ya yi aiki tuƙuru tsawon shekaru don gina kasuwancinsa amma ya ƙare ya rasa wannan jarin cikin daƙiƙa.

KU KUMA KARANTA: An Yi Gobara A Wani Sashen Gidan Sheikh Gumi A Kaduna

“Ina jin raɗaɗin duk wanda wannan lamari ya shafa. Ina jajanta ma dukkan ku. Ina mai ƙira gareku cikin ladabi da girmamawa da ku nutsu da hakuri. Nasan yadda kuke ji kuma insha Allahu tuni gwamnatin jihar Borno ta fara daukar wadannan matakai domin gyara lamarin.

“Na amince da sakin Naira biliyan 1 a matsayin agajin gaggawa don tallafa wa wadanda bala’in ya rutsa da su cikin gaggawa domin mun san cewa wasu daga cikinsu na iya samun wahalar rayuwa nan da ‘yan kwanaki masu zuwa.

Mutane da yawa sun dogara ga kasuwancin yau da kullun don biyan bukatun kansu. “Muna kafa kwamitin tantancewa wanda zai kunshi mutane masu mutunci daga cikin al’ummarmu da suka hada da wakilan wadanda abin ya shafa, domin mu gaggauta tantance irin barnar da aka yi, da kuma daukar cikakken jerin wadanda abin ya shafa da kuma asarar da suka yi.

Zan kuma yi taro da shugabannin kasuwar da wakilan waɗanda abin ya shafa. “Zan ga shugaban ƙasa kuma in nemi taimakon shi kan yadda zan samu tallafi ga waɗanda abin ya shafa.

“Za kuma mu kai ga sauran cibiyoyin jin kai don neman taimako. In sha Allahu zamu ɗauki kwararan matakai na hana sake afkuwar wannan bala’in gobara da ya faru a shekarun baya. “Ina so in yi kira ga kowa da kowa domin ya samu nutsuwa, na san yadda kuke ji.

Ina jin zafin, kuma za mu tallafa muku ta duk hanyar da za mu iya, insha Allahu. “A halin yanzu, ina kira gare mu da kada mu sanya siyasa a wannan lamari mara dadi. Na gane cewa lamarin yana faruwa a lokacin siyasa, amma duk mun san kasuwar litinin ta fuskanci bala’in gobara a lokutan baya kuma wannan abin bakin ciki ne.

“Dole ne mu nemo hanyoyin da za mu tabbatar da cewa wannan bala’in gobara bai sake faruwa ba kuma za mu yi aiki tare don tabbatar da hakan.”

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Gwamna Buni ya jajantawa gwamnati da jama’a Borno kan gobarar kasuwa | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gwamna Buni ya jajantawa gwamnati da jama’a Borno kan gobarar kasuwa - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like