Gwamna Buni ya jajantawa gwamnati da jama’ar Borno kan gobarar kasuwa

4
267

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Borno, kan gobarar da ta tashi a kasuwar litinin.

A wata sanarwa da Mamman Mohammed ya sanya wa hannu, Darakta Janar na yaɗa labarai da hulɗa da manema labarai, ya bayyana cewa Gwamna Buni ya bayyana a matsayin abin bakin ciki, abin takaici,akan gobarar da ta tashi a kasuwar, cibiyar kasuwanci da ke samar da hanyoyin rayuwa ga mutane da dama.

“Abin baƙin ciki ne cewa wannan lamari ya faru ne a daidai lokacin da jama’a ke farfaɗo da rayuwarsu ta fuskar tattalin arziki daga doguwar kalubalen tsaro da ya durkusar da ɓangaren tattalin arziki a yankin Arewa maso Gabas.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya bada sanarwar tallafin naira biliyan ɗaya ga waɗanda gobarar kasuwa ta shafa a Maiduguri

“Gwamnati da al’ummar jihar Yobe suna tare da ku a wannan lokaci mai wuyar gaske, kuma ku yi addu’a ga Allah (SWT) Ya cika muku rashi ta hanyoyinsa mafi kyau. “Muna jin zafin wannan rashi na bakin ciki, muna tare da ku, muna rokon Allah ya saka masa da mafificin alheri”.

“A matsayinmu na masu imani muna da cikakken imani cewa Allah Madaukakin Sarki yana da iko a kan komai kuma zai ga wadanda abin ya shafa a cikin wannan mawuyacin lokaci da zafi,” in ji Buni.

Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikan waɗanda abin ya shafa, ya ba su goyon baya don daukar rayuwarsu, ya kuma daƙile duk wani abu da zai faru nan gaba.

4 COMMENTS

Leave a Reply