Connect with us

Tsokaci

Muhimmmancin Makarantun Kimiya Da Fasaha Da Yadda Za Su Cicciba Najeriya Sama

Published

on

Daga; Auwal Ahmed Ibrahim (Goronyo)

KAMAR yadda kusan kowane dan Najeriya ya sani ne cewa ilmin makaratun firamari a Najeriya musamman na Gwamnati ta zama tamkar mushan gizagi a wasu garuruwa inda mafi yawan dalibai a makarantu ba su da gurin zama, babu ofisoshin malamai ga kuma rashin makewayoyi masu kyau da tsafta duk da irin makudan kudade da gwamnatoci suke warewa a kowane mataki, to amma wannan bai hana ilmin makarantun kananan makarantun gwannati tabarbarewa ba.

A wata hira da aka yi da shugaban hukumar Ilmin Kimiya da Fasaha ta kasa, Farfesa Idris M. Bugaje a gidan rediyon Rhythm FM, Abuja, ya bayyana cewa inda ba don gwagwarmaya da jan tunga da kungiyoyin malaman makarantun manyan gaba da sakandire suke yi ba da ilmin jami’o’in Najeriya ya zama ba banbanci da ilmin makaratun firamari badan.

Sai dai kuma masana na ganin kudaden da gwannati ke warewa bai wuce cikin cokaliba na abun da ya kamata ta kasheba wajan farfado da ilimi musamman a matakin farko a kasar nan.

Bukatar Hukumar kyautata Ilimi da kimiya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) shi ne ga kowace kasa ta ware kaso kashi 26 na kasafin kudin ta ga ilimi. Amma a Najeriya a shekara ta 2021 kaso biyar zuwa shida aka ba bangaran ilimi, hakazalika a shekarata 2022 da ake ganin ya kamata a ma ilimi rikon dan amaryar, Inda sashen Ilimin ya sami kashi 14 cikin dari dan farfado da ilimin bayan irin jibgar da annobar Cuta mai Shake Numfashi (Corona Virus) ta yi ma ilimin a kafatanin fadin duniya.

Ilimi baya tafiya yadda ya kamata har sai malamai sun sami kulawa amma mafi akasarin malaman Najeriya cikin tsaka mai wuya suke inda su kan kasance a tsakiyar kura da siyaki.

Wasu malamai ko a jami’o’i ba su da ofisoshin da za su zauna su gudanar da ayyukan su, haka tashin gwauron zabi da rayuwa ta yi ta jefa malamai da yawa cikin ni’yasun kuncin rayuwa duk da irin kokarin su na tabbatar da sun bayar da ilimi kamar yadda ya kamata wajan sauke nauyin da aka daura masu.

Kamar dai yadda aka sani ne cewa ilmi shi ne gishirin rayuwar da yake saka rayuwa dadi, badan malamai ba, da rayuwa ta kara muni da kunci. Ilmi shi yake taimakon kowane dan-adam ya gina rayuwarsa har ya haskama wasu fitila domin shi kansa ilimi kan samar da aiki ga dunbin al’ummar kasa, sai dai wani kuskure da yake karama kwabar Najeriya ruwa a bangaran ilimi shi ne wuce makadi da rawa da ake yi wajan yawaitar jami’o’i a Najeriya fiye da makarantun kimiya da fasahohi wadanda manufar su shi ne koyar da sana’o’in hannu a zahiri.

Farfesa Idris M. Bugaje yana da tunani da yakini na cewa idan makaratun kimiya da fasaha suka fi yawa kuma aka inganta su a kasar nan, za a sami raguwar fitintunun da su ka ma kasar daurin laimon minti, haka kuma ayyuka za su wadatu a kasar har jama’ar kasar su fantsama cikin duniya domin fafutukar neman halaliyar su a wasu kasashe cikin kima da kulawa.

A Najeriya, kiyasi ya nuna cewar akwai makarantun kimiya da fasaha guda 69 a inda ake da kimanin jami’o’i guda 170 wanda abun da ake gani wannan shi ne barin reshe a Kama ganye.

A cewar Farfesa Bugaje, kwalejojin kimiya da fasaha suna da kaifi biyune wajan Cicciba kasa ga tudun muntsira baya ga horar da dalibai ilmi, kuma akwai horo da sukan iya ba ‘yan kasuwa masu aikin hannu dan samun Takardun shaidu da za su iya aiki da su a ko’ina a fadin duniya koda kuwa ma ba su taba shiga aji ba. Haka kuma a ka’ida daliban makarantun kimiya da fasaha ya kamata su fi yawa dan kuwa a duk karkashin wani shugaba a gurin aiki da ake bukata a ma’aikata ko gurin aiki ana bukatar masu tallafawa guda biyar wadanda suka sami horo daga kwalejojin kimiya da fasaha.

Ko shakka babu, ilimin kimiya da fasaha shi ne zai iya tsayar da Najeriya a kan bigiran kasashen duniya wadanda suka tsaya da dugadugin su amma samuwar haka kan iya tabbatuwane kadai idan gwannati ta bayar da fifiko da kulawa ga makarantun kimiya da fasaha a kasar nan dan tabbatar da Najeriya kasar da zata dinga cin gashin kanta ba a matsayar saniyar tatsa ba.

Hukumar Kula da Makarantun Kimiya da Fasaha ta Najeriya, NBTE ita ce madogara a daidai wannan lokaci da Najeriya take kokarin samun mafuta ga matsalolin da suka mata katutu da makoko.

Kamar yadda masanan ilmi da addini suka tabbatar cewa tsaro baya samuwa a tsakanin al’ummar da yunwa take ci kamar wutar daji. A daidai irin wannan lokacin da Najeriya take kukan targade da karaya, gwannati ba zata iya share ma jama’a hawaye ba har sai kowa ya mike dan yakar talaucin da yake bude da baki kamar zaki. Koyan sana’a yana da kyau amma zuwa makarantar da zata ba da shaidar koyan aiki shi ne mafi a’ala.

Fasalin manhajar karatun makarantun kimiya da fasaha shi ne yake bayar da sa’ar baro tsuntsu biyu da dutse daya, tun mutun yana dalibi yakan iya fara cin moriyar karatun sa kafin kammalawa, in kuwa ya kammala ya samu takardar yakan iya samun aiki.

Damar da NBTE take da shi na horar da masu sana’o’in hannu da bayar da shaida, abu ne da zai tsayar da kasar nan a kan turbar mun tsira ga masu sha’awar kara daukaka kan su a sana’o’in su domin kuwa a dukkanin kowace sana’a, buncike shi yake kara daukaka a kanta.

Iyaye da dalibai, ya kamata su fahimci, makarantun kimiya da fasaha ya kamata su runguma domin cigar da kasar nan gaba da kuma samun dogaro da kai domin dai bukatar maje haji sallah.

Sai dai kuma dan rungumar wannan kudiri sai fa gwannati ta gane muhimmanci da alherin da ke ciki tumbul tartare da makarantun kimiya da fasaha wajan gina kasa da gina al’umma. Haka samar da kayan koyan karatun da horarwa za su taimaka gaya wajan fardodo da kimar makarantun kimiya da fasaha a Najeriya, sannan da so samu ne daliban makarantun kimiya da fasaha in basu zama wadanda za su dunga amsar albashi mafi tsoka ba, to su zama daidai da dukkanin daliban jami’o’i a kowane fanni kila ko shakka wannan ne zai kara kima da martabar makarantun kimiya da fasaha a Najeriya.

Auwal Ahmed Ibrahim (Goronyo)
Malami ne a Kwalejin Kimiya Da Fasaha Ta Kaduna A Sashen Koyar Da Aikin Jarida

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

Zaɓen 2023: Matsayar kafafen yaɗa labarai na Arewa, daga Ɗan Agbese

Published

on

Yayin da ‘yan Nijeriya ke shirye-shiryen zaben shugaban ƙasa da na gwamnoni da ‘yan majalisu a zaben 2013 mai zuwa, kafafen yaɗa labarai na Arewacin Najeriya sun ɗauki matsayar bada shawarwari, domin saita alƙiblar masu kaɗa ƙuri’a na yakin, da kuma masu neman madafun iko, a wani ɓangare na irin gudunmuwar da za su iya bayar a zaɓen.

Kwanan ne hukumar ƙididdiga ta ƙasa, ta fitar da mizanin matsanancin talaucin da ake fuskanta a Nijeriya, kuma sakamakon abin Allah-Wadai ne, domin rahoton ya nuna aƙalla ‘yan Nijeriya miliyan 133, kwatankwacin kashi 63 cikin 100 duk matalauta ne, kuma mutane miliyan 86, kwatankwacin kashi 65 cikin 100 ‘yan Arewa ne.

Don haka ba abin mamaki ba ne, idan aka kwatanta yankin Arewa, wanda shi ke da rinjayen yawan al’umma, a matsayin yanki mafi haɗarin zama a faɗin kasar nan.

Don haka ya zama wajibi, duk masu hanƙoron neman shugabanci a zaɓen shekara ta 2023, su fito fili, su bayyana shirin da su ke da shi na ceto waɗannan tarin mutanen da ke fama da ƙuncin rayuwa, mutanen da rashi ya yi wa ƙatutu, musamman ta fuskar kiwon lafiya, da rashin isasshen abinci da kuma muhalli.

Wannan fa kari ne ga adadin matalautan da ke zaune a yankunan karkara, inda mazauna yankin ke da kashi 72 cikin 100, akasin kashi 42 na wadanda ke zaune a cikin birane.
Daya daga cikin musabbabin ta’azzarar matsanancin talauci musannan a yankin arewa, shi ke ta’azzarar matsalar rashin tsaro.

Daga matsalar Boko Haram, da rikicin manoma da makiyaya, sai kuma ayyukan ta’addancin ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane. Kiri-kiri, yanki ya zama tamkar mayanka.

Sai dai ba abin mamaki ba ne, kasancewar talauci ya janyo matasan da ba su da aikin yi ana ɗauka su aiki a matsayin ‘yan daba, ko kuma ‘yan ta’adda zaune tsaye.
Mu fara da yankin Arewa maso Gabas, inda ta’addancin Boko Haram ya mamaye, duk da dai dakarun sojin Nijeriya sun ci galabar mayakan a wasu yankunan, zuwa yankin tsakiyar Nijeriya, inda rikicin manoma da makiyaya ya yi wa dabaibayi, da kuma yankin arewa maso Yamma, inda ‘yan bindiga su ke cin karen su babu babbaka, ana ji ana gani, ana ta zubar da jinin mutane tsawon shekaru 15 a yankin Arewa, tun bayan kisan da ‘yan sanda su ka yi wa shugaban ‘yan Boko Haram Muhammad Yusuf.

Haka nan dai rashin tsaro ya yi ta ta’azzara har zuwa shekara ta 2015, wanda shi ne musabbabin zaɓen gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

Sai dai abin bakin cikin shi ne, tsawon shekaru bakwai ayyukan ta’addanci sai ma abin da ya yi gaba, lamarin ma sai ya zo da dalailai daban-daban.

Tuni dai rahotanni sun bayyana cewa, a jihohin Zamfara da Sokoto, ‘yan bindiga ke tsara wa ‘yan siyasa wuraren da za su gudanar da gangamin yakin neman zabe, da kuma lokacin da za su yi, wannan ba ƙaramin haɗari ba ne, kuma idan har wannan baƙin lamarin ya cigaba a haka, ina mai tabbatar maku cewa babu ranar ƙarewar ayyukan ‘yan bindiga, musamman a ce wai su ke ba ‘yan siyasa kariya.

Lamarin nan fa ba abin lamunta ba ne jama’a, duk wanda ya san ya isa, kuma ya na neman mukamin siyasa, dole ya ƙ hoiudiri kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga, ba wai ya kulla alaka da su ba.
Ayyukan ta’addaci dai sun tagayyara al’umma, kuma kalaman yadda za a kawo karshen lamarin ne kawai zai iya sama wa masu neman mukaman siyasa kuri’un masu zabe.
Muna kuma gargadin masu kada ƙuri’a su yi taka-tsatsan da duk wasu ‘yan siyasar da aka san su na hulda da ‘yan bindiga.

Wani bangare na matsalolin da rashin tsaro ya haifar kuma shi ne, ilimin yara ya shiga halin ni-‘yasu, domin a yankin Arewa, ilimin yara ya faɗa cikin mawuyacin hali.
Daga fashin jirgin ƙasa, kiri-kiri an kassara bangaren ilimi. Misali, a shekara ta 2020, ɗalibai 300 aka sace a Kwalejin Kimiyya da ke Kankara a jihar Katsina, sannan a cikin watan Mayu na shekara ta 2021, ɗaliban Islamiyya 130 aka sace daga wata makarantar Islamiyya ta Salihu Tanko da ke garin Tegina a jihar neja.

Sannan duk a cikin watan Mayu na shekara ta 2021, an sace dalibai 126 daga wata makarantar kiristoci ta Bethel Baptist da ke Damishi a jihar Kaduna, yayin da a cikin watan Yuni na shekara ta 2021, aka sace dalibai mata 112 daga Sakandaren Gwamnatin tarayya da ke Yauri a jihar Kebbi, baya ga daliban jami’ar Greenfield da aka sace a jihar Kaduna, da sauran matsaloli makamanta wannan ga su nan ba iyaka.

Wasu daga cikin ‘yan matan da aka sace ma tuni sun haifa wa ‘yan bindiga ‘ya’ya a cikin dazuzzuka, kuma an bar iyaye su san yadda su ka yi da ilimin ‘ya’yan su mata. Wannan fa ya na daga cikin musabbabin ta’azzarar adadin yaran da ba su zuwa makaranta.

Duk wani mai neman madafun iko ba sai an yi nisa ba, domin duk kalubalen da ake fuskanta an san su, don haka duk wani matakin riga-ƙafi ba abu ne mai wahala ba, ‘yan Nijeriya maganin matsalolin da su ke addabarsu su ke buƙata a yanzu.

Yankin Arewa dai bai tsaya a kan matsalar ‘yan bindiga kawai ba, ya zama dandalin miliyoyin ‘yan gudun hijirar da ‘yan ta’adda su ka tagayyara, sun rasa muhallan su, rayuwar su ta shiga garari, don haka akwai buƙatar ɗaukar matakin gaggawa, domin a maida su garuruwa da muhallan su na asali.

Babu wani dan siyasar da zai zo gobe ya ce bai san yadda wannan bala’in ya riski mutane ba, don haka ba su da wata hujjar neman shugabanci, matuƙar ba su da shirin kawo karshen manyan kalubalen da jama’a ke fuskanta.

Kafafen yaɗa labarai na yankin arewa sun yi gargadin yiwuwar haramta ma wannan tarin bayin Allan ‘yan cin jefa ƙuri’un su, don haka su ka ja hankalin hukumomin tsaro su tabbatar sun ba ‘yan gudun hijira kariya, hukumar zaɓe kuma ta shirya yadda za a ba su damar jefa ƙuri’a domin zaɓen wanda su ke so ya shugabance su.

Kafafen yaɗa labaran, sun kuma yi Allah-Wadai da salon gangamin yaƙin neman zaɓen da ake yi a Nijeriya, inda ‘yan siyasa ke cin zarafin abokan hamayya maimakon maida hankali a kan abin da zai amfani al’umma.

‘Yan siyasa sun gwammace amfani da kalaman cin zarafi, su na amfani da addini, maimakon su maida hankali a kan matsalolin da al’umma ke fuskanta,
ɓangaren ilimi dai ya shiga tasku, inda har yanzu rikici tsakanin kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU da gwamnatin tarayya bai ƙare ba.

Aikin yi ya gagari miliyoyin ɗaliban da suka kammala jami’a a Nijeriya.
Akwai bukatar a samar da shirye-shiryen yadda za a farfado da tattalin arzikin mu, a samar da ayyukan yi ga aƙalla matasa miliyan 30 da ke zaman kashe wando.
Ba mu bukatar masu ɓaɓatun fatar baki ko wadanda ba su ɗauki rayuwar jama’a da mahimmanci ba, muna bukatar ƙwararan shirye-shirye gabanin zaɓen shekarar 2023.

Babu abin da yankin arewa ke buƙata a daidai wannan lokacin, illa ƙwaƙƙwaran shirin kawo karshen matsanancin talauci da yunwa da takaicin da al’ummomin yankin ke ciki.

Don haka muna bukatar a inganta yankin Arewa da ma Najeriya baki ɗaya kowa ya samu yalwa.

‘Yan Nijeriya dai su na sa ran a gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a shekarar 2023.

Wani abin burgewa shi ne, dokar zabe ta shekara ta 2022, ta samar da Na’urar tantace masu kaɗa kuri’a ta BVAS, inda za a rika tura sakamakon zaɓe kai tsaye ta yanar gizo.

Ga dukkan alamu dai, da kuma rawar da hukumar zabe ta taka a zabubbukan jihohin Anambra da Ekiti da Osun, amfani da wadannan na’urorin ya tabbatar da cewa zai yi wahala a iya yin maguɗin zaɓe, lamarin da ya ba ‘yan Nijeriya ƙwarin giwar cewa ba za su yi asarar kuri’un su ba.

Muna kuma jan hankalin masu kaɗa ƙuri’a, su yi amfani da wannan dama da hukumar zaɓe ta samar, wajen amfani da na’u’rorin zamani yayin gudanar da zaɓe, ta yadda nan gaba hatta siyasar kuɗi za ta zama tarihi a Nijeriya.

Wannan, matsayar ƙungiyar kafafen yada labarai ta Arewacin Najeriya Kenan, ɗauke da sa hannun shugaban ta Dan Agbese, da sakatariyar ƙungiyar Zainab Suleiman Okino.

Continue Reading

Tattalin arziƙin ƙasa

Abin da ya kamata ku sani kan sabbin dokokin hada-hadar Naira

Published

on

Babban bankin Najeriya (CBN) ya sanar da sabbin dokokin hada-hadar Naira wadanda zasu fara aiki a farkon shekarar 2023 a ranar tara ga watan Janairun shekarar (9/01/2023).

Neptune Prime Hausa ta kawo maku abubuwan da ya kamata ku sani game da haka;

1-Duk wanda zai cire kuɗi a asusun ATM, Naira dubu ashirin kawai zai iya cirewa a rana ɗaya,haka kuma, Naira dubu ashirin kawai mutum zai iya cirewa a rana a asusun POS.

2- A mako guda Naira dubu ɗari kacal mutum zai iya cirewa a ATM ko a POS

3-Takardun Naira 200 sune mafi girman takardun kuɗi da za a dinga sanyawa a ATM

4- Mafi yawan kuɗin da mutum zai iya fitarwa a cikin banki a wuni shine Naira dubu ɗari (₦100,000), Ma’aikata kuma mafi yawan kuɗin da za ta iya cira shine Naira dubu ɗari biyar.

KU KUMA KARANTA:Shugaba Buhari ya kaddamar da sabbin takardun kuɗi

Idan da akwai dalilin da zai sanya mutum ko masana’anta ta cire kuɗin da ya haura adadin da aka ƙayyade za a biya kuɗin kwamasho, idan mutum ne zai cire sama da adadin ba kamfani ko ma’aikata ba, zai biya kudin kwamasho na kashi biyar cikin dari da adadin kudin da zai cire wato 5%.

Idan kuma kamfani ne ko ma’aikata, zasu biya kudin kamisho na kashi goma cikin ɗari wato 10% na abinda zai cire.

  1. Dukkanin kuɗin da za’a cire ta hanyar wani ya baka Cheque wato 3rd Party Cheque na kudin da ya haura naira dubu hamsin (₦50,000) dole sai a kanta za a cire.
Continue Reading

Kasashen Waje

Yadda Sarkin Farisa ya yanke hukuncin feɗe fatar alƙali da ransa

Published

on

Wannan wani zane na karni na 16, dake nuna fatar jikin wani alƙali da yayi rashin daraja, me suna Sisamnes, a shekara ta 500BC.

Sisamnes ya kasance alƙali mai cin hanci da rashawa a lokacin Cambyses ll a Farisa. An gano cewa ya karbi cin hanci a kotu kuma ya yanke hukuncin da bai dace ba.

Saboda haka ne sarki ya ba da umarnin a kama shi da laifin cin hanci da rashawar, sannan ya ba da umarnin a yanke fatarsa da ransa kafin a kashesa, domin yaji raɗaɗin cirewar.

Kafin yanke hukuncin, sarki ya tambayi Sisamnes wanda yake so ya nada a matsayin magajinsa. Sisamnes, a cikin son kansa, ya zaɓi ɗansa, Otanes. Sarki ya yarda, kuma ya nada Otanes ya maye gurbin mahaifinsa.

Bayan an zartar da hukuncin, Sarkin ya kuma ba da umarnin a yi amfani da fatar Sisamnes da aka cire, don lulluɓe kujerar da sabon alkali zai zauna a kotu. Yayi hakan ne domin tunatar da shi illar cin hanci da rashawa.

Wannan yasa dole Otanes, ya dinga tunawa a koyaushe, yana zaune a kan fatar mahaifinsa da aka kashe. Wannan ya taimaka wajen tabbatar da adalci da daidaito a cikin dukkan sauraren ƙararsa, shawarwarinsa da hukunce-hukuncensa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like