Azumin watan Ramadan
Gwamnatin Yobe ta ware miliyan 73 don ciyar da masu azumi a watan Ramadan
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/04/IMG-20230407-WA0166.jpg)
Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya amince da kashe Naira miliyan 73 don ciyar da marasa galihu a ƙarƙashin shirinta na ciyar wa a watan Ramadan na shekarar 2023.
Alhaji Mala Musti kwamishinan harkokin addini na jihar ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Damaturu. Ya kuma bayyana cewa samar da dafaffen abinci da gwamnatin jihar ke yi ga mabuƙata a cikin watan Ramadan al’ada ce tun shekarar 1999.
Kwamishinan ya ce tuni ma’aikatar ta kai buhunan shinkafa 1,050 domin shirin, inda ya ce za a ƙara karbar buhunan shinkafa domin ci gaba da aiwatar da shirin. “Kuɗaɗen da gwamnati ta amince da shi, shi ne Naira miliyan 73, za a yi amfani da su ne wajen sayan raguna da kayan dafa abinci a cibiyoyin ciyar da abinci 67 da aka samar a jihar.
KU KUMA KARANTA: Za mu ci gaba da takatsantsan wajen amfani da dukiyar jama’a – Gwamna Buni
“Mun shirya sanya jami’an mu da za su zagaya domin duba duk wuraren da ake ciyar da abinci; ba za mu iya barin shi haka don mutane su je su yi duk abin da suke so ba, ”in ji Musti.
Ya yi kira ga masu hannu da shuni da su shiga cikin shirin, inda ya ce akwai lada mai yawa wajen ciyar da gajiyayyu musamman a watan Ramadan.
Ya ƙara da cewa, gwamna Buni ya kuma amince da naira miliyan 30 a matsayin alawus ga malaman addinin musulunci domin gudanar da ayyukan ibada daban-daban a cikin lokutan azumi.
Azumin watan Ramadan
Ba a ga watan sallah a Najeriya ba
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/04/IMG-20240408-WA0008.jpg)
Kwamitin duban wata na fadar mai martaba Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ce ba a samu ganin jinjirin watan Shawwal ba a yau Litinin, 29 ga watan Ramadan.
Wata sanarwa ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin Farfesa Sambo Wali Junaidu ta ce Sarki Musulmi kuma shugaban majalisar koli ta harkokin addinin musulunci a Najeriya ya amince da rahoton kwamitin.
KU KUMA KARANTA: Ba a ga watan ƙaramar Sallah ba a Saudiyya
Saboda haka ya yi matsaya cewa watan Ramadan zai cika kwanaki 30 kuma ranar Laraba 10 ga watan Afrilu, ita za ta kasance 1 ga watan shawwal kuma ranar sallah karama a Najeriya
Ba wannan ne karon farko da ake yin Azumi talatin ba a Najeriya.
Azumin watan Ramadan
Ba a ga watan ƙaramar Sallah ba a Saudiyya
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/04/FB_IMG_1712514971011.jpg)
Hukumomi a Saudiyya sun ce ba a ga watan Shawwal ba a ƙasar ranar Litinin, 29 ga watan Ramadan shekarar 1445, daidai da takwas ga watan Afrilu, 2024.
Sun bayyana haka ne a sanarwar da aka wallafa a shafin Haramain wanda ke kula da masallatai masu tsarki.
Hakan na nufin ba za a yi ƙaramar Sallah sai ranar Laraba, 10 ga watan Afrilu.
Azumin watan Ramadan
Watan Ramadan: Shaikh Zakzaky ya raba buhunan kayan abinci ga mabuƙata (Hotuna)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0019.jpg)
Daga Ibraheem El-Tafseer
Jagoran Harka Islamiyya a Nijeriya, waɗanda aka fi sani da Shi’a, Shaikh Ibraheem Yaqoub Al-Zakzaky ya raba buhunan kayan abinci ga mabuƙata kamar yadda ya saba kowace shekara.
Shehin Malamin ya saba raba buhunan shinkafa, Hatsi da Masara ga al’umma mabuƙata saboda falalar watan Azumin Ramadana mai albarka.
Kamar kowace shekara, a bana ma, ƙanin sa ne, Malam Badamasi Yaqoub Zakzaky ya jagoranci raba wa ɗin, a birnin Zariya da ke jihar Kaduna, a yau Laraba.
Ga hotunan a nan:
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0007-1024x576.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0008.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0006-1024x768.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0012-1024x768.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0018-1024x768.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0013.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0017.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0011-1024x768.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0010-1024x576.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0009-1024x768.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0016.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0015-1024x768.jpg)
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG-20240313-WA0014.jpg)
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai10 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: Saboda bikin sallah: Gwamnan Kebbi ya ba da umarnin a biya albashin watan Afrilu | Neptune Prime Hausa
Pingback: Masallacin ƙasa na Abuja ya bayar da tallafin abinci ga ‘yan gudun hijira 400 | Neptune Prime Hausa
Pingback: Masallacin ƙasa na Abuja ya bayar da tallafin abinci ga ‘yan gudun hijira 400 - LEGEND FM DAURA