Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Lasisin Makarantu Masu Zaman Kansu

0
340

 Daga Rabo Haladu

Gwamnatin Jihar Kano ta dakatar da lasisin dukkan makarantu masu zaman kansu har sai an tantance su.

Kwamishinan Ilimi na Kano Sanusi Said Kiru ne ya sanar da hakan a yayin ganawa da manema labarai.

Lamarin na zuwa ne yayin da aka gurfanar da mai makarantar Noble Kids a kotu, wanda ake zargi da kashe Hanifa Abubakar mai shekara biyar a makarantar tasa.

Ya ce za a kafa wani kwamiti na musamman da zai tantance makarantun sannan za ta fitar da matakan da za a yi amfani da su wajen tantance makarantu a jihar.

Kazalika ya ce dukkan makarantun da ba su cika sabbin ka’idojin da za a saka ba, sun tafi kenan – ba za a buɗe su ba

Gwamnatin Kano ta dakatar da lasisin makarantu masu zaman kansu

 Daga Rabo Haladu

Gwamnatin Jihar Kano ta dakatar da lasisin dukkan makarantu masu zaman kansu har sai an tantance su.

Kwamishinan Ilimi na Kano Sanusi Said Kiru ne ya sanar da hakan a yayin ganawa da manema labarai.

Lamarin na zuwa ne yayin da aka gurfanar da mai makarantar Noble Kids a kotu, wanda ake zargi da kashe Hanifa Abubakar mai shekara biyar a makarantar tasa.

Ya ce za a kafa wani kwamiti na musamman da zai tantance makarantun sannan za ta fitar da matakan da za a yi amfani da su wajen tantance makarantu a jihar.

Kazalika ya ce dukkan makarantun da ba su cika sabbin ka’idojin da za a saka ba, sun tafi kenan – ba za a buɗe su ba


Leave a Reply