Connect with us

Uncategorized

AN KADDAMAR DA MAGAJIN BALARABE MUSA A PRP

Published

on

MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI

AN bayyana jam’iyyar PRP da cewa ita ce jam’iyyar da babu wani bangare a cikinta ko kadan.

An bayyana hakan ne a wajen babban taron kaddamar da Magajin Balarabe Musa da nufin ya jagoranci jam’iyyar PRP domin ya Gaji mahaifinsa 
Kuma duk wanda ko wasu da suke cewa akwai bangare to sune bangaren, amma PRP a dinke take guda daya ce ba wani bangare ko kadan.
Shugaban jam’iyyar PRP na karamar hukumar Soba Alhaji Isa Soba,ya ce duk dan shekara Talatin ko Talatin da biyar bai san PRP ba sai dai a yanzu za a koya masu me ake nufi kuma meye PRP, sai dai yan shekaru 50 zuwa 60 dune suka san meye PRP.
Alhaji Isa Soba, “abin da aka fadi a game da halaye Malam gaskiya ne,PRP its ce kadai jam’iyya a Afrika ba wai a Nijeriya ba
Mu muka nemi a ba mu wani daga zuri’arsa ya zama Khalifa, ayi hakuri domin hakurin ya kawo har a yanzu muke tare da tafiyar nan har yanzu.
PRP bata da wata matsala sai dai shure kawai, a hada kai, muna fatan za a yi hakuri 
Auwal Ibrahim daga Kano shugaban tabbatar da canji irin na gaskiya a kasa baki daya
“Duk wanda ya kasance dan PRP mai akida ta gaskiya domin son a samu canji dai dai yake da mutane miliyan daya”, inji Auwal.
“Ya kara da cewa muna nan a cikin hasken PRP har abada domin in mun mutu wasu ne za su ci gaba daga inda aka tsaya”.
“Katin jam’iyya ake Sayarwa a samar da Ofisoshi da sauran hidimar jam’iyya domin kowa ya zama da cikakke ba Bawa ba,a 1979 PRP ta sa an samu wakilcin kowa ne dan kasa a Najeriya, sai mun amince a cikin Rubin zuciyarmu cewa za mu iya kawo zaben Najeriya”.
Ya bayyana Malam Kassimu da cewa zai iya jawo nasarar da kowa ke bukata domin ya na da jajircewa da son PRP, domin a kan haka ne Malam Aminu Kano ya ce ya na ganin haske a can nesa to wannan haske zamu kai hare shi.
Honarabul Kassimu Balarabe Musa ya ce hakika wannan babban takalmin da aka ba ni ya fi karfi na amma duk inda aka ce an baka wani matsayi to ya dace ka daure ka rike domin alkairi ne.
“Hakika wannan matsayi su Soba ne suka ba ni sai fatan Allah ya ba ni ikon rikewa domin kasa da al’ummarta su amfana”.
Ayi hakuri ga zabe ya zo don haka a hada kai ayi tafiya daya shugabanni daya ba tare da samun Rabe Rabe ba.
Jama’a ayi hakuri abi Alhaji Falalu Bello wanda shi ne Malam Abdulkadir Balarabe Musa ya dauka a cikin mutum miliya ya bashi domin ya ga cancantarsa
“Kuma Falalu Bello shi ne sunansa yake a wurin INEC don haka ina kan Gwiwa a kasa 
Kassimu ya kuma yi kira ga Malam Nasiru Ahmad El- rufa’i ya shigo cikin jam’iyyar PRP domin wannan jam’iyya ta PRP ita ce gidan aiki
Ya kuma yi godiya ga yayan jam’iyyar APC da suka zo taron PRP domin mu a ciki  PRP PRP Adam ya fi komai muhimmanci ko talaka ko me kudi
Ayi hakuri da abin da ke kasa azo a goyi bayan Alhaji Falalu Bello a matsayin shugaban PRP na kasa. 
“Ina godiya ga mutane  da suka ba ni wannan jagoranci duk da ina ta kaucewa amma dai suka ce sai ni
Mista Mark ya ce a matsayinsu na shugabannin jam’iyya a Jihar Kaduna za su bayar da hadin kai da goyon baya.
Mataimaki Tan…ya hi kira ga yayan jam’iyyar PRP da su yi hakuri a tafi tare domin duk kowace jam’iyya ana samun wannan don haka ayi hakuri, PRP daya ce gida daya ne kuma guda daya ce.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Addini

Ranar Lahadi ce 1 ga watan Muharram – Sarkin Musulmi

Published

on

Ranar Lahadi ce 1 ga watan Muharram - Sarkin Musulmi

Ranar Lahadi ce 1 ga watan Muharram – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad III, ya bayyana cewa gobe Lahadi ce za ta zama 1 ga watan Muharram na sabuwar shekarar Musulunci ta Hijira 1446.

Shugaban kwamitin da ke bai wa Sarkin Musulmi shawara kan harkokin addini, Farfesa Sambo Wali Junaid ne bayyana hakan a ranar Juma’a.

Farfesa Junaid ya ce kwamitin haɗin gwiwa da kwamitin ganin wata na Najeriya sun tabbatar ba a samu ganin watan Muharram na shekarar 1446 a ranar Juma’ar ba, abin da ke nuna ranar Asabar za ta zama 30 ga watan Zhul Hijja na shekarar 1445.

KU KUMA KARANTA: A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

“Sakamakon haka, Asabar [6 ga watan Yuni] ta zama 30 ga watan Zulhijja 1445…Lahadi kuma [7 ga Yuni] ta zama 1 ga watan Muharram 1446,” a cewar shugaban kwamitin ganin wata na fadar sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali cikin wata sanarwa.

“Sarkin Musulmi na taya Musulmin Najeriya murna [sabuwar shekara] da kuma roƙa musu alheri da taimakon Allah,” in ji sanarwar.

Sarkin Musulmin ya roƙi jama’a su ci gaba da addu’ar zaman lafiya da samun ci gaba a ƙasa baki ɗaya.

A tsarin Musulunci, kowane wata kwana 29 ne amma idan aka kasa ganin jaririn sabon wata akan cika watan zuwa kwana 30.

Continue Reading

Addini

Biyan kuɗin shiga Itikafi a Masallatai bidi’a ce — Sheikh Maqari

Published

on

Babban Limanin Masallacin Juma’a na Ƙasa, Farfesa Ibrahim Maqari ya yi tir da tsarin da wani Masallaci a Legas ya fito da shi na biyan kuɗi kafin mutum ya yi ibadar Itikafi a cikinsa.

Limamin ya bayyana ɓacin ransa na wannan sabon abu da Masallacin ya fito da shi ne tare da yin sharhi mai tsawo kan haka a yayin tafsirinsa da ya ke yi a Babban Masallacin Juma’a na Ƙasa da ke Abuja.

Shehun Malamin ya kwantanta wannan mataki da masallacin na Legas ya fito da shi a matsayin wata sabuwar fitina a addini wacce ta fi kowacce bida’a muni a wannan zamani.

Wanda a cewarsa hakan zai iya haifar da fushin Allah kan wannan al’umma saboda kasuwantar da ɗakinSa ne wanda wasu addinai ke yi.

“Masallaci ɗakin Allah ne kuma da zarar mutum ya shiga, duk wani girma da ɗaukaka da muƙami da matsayi ya kare bakin kofa inda ya ajiye takalminsa.

“Duk wanda ke cikinsa daidai yake da kowa ba tare da banbancin mai shi da maras shi ba na dukiya ko matsayi.

“A inda zai iya zama a ko’ina kuma kusa da kowa. Amma sa kuɗi zai buɗe kofar nuna banbanci da matsayi wanda hakan ba musulunci bane,” in ji shi.

A yayin da yake amsa tambayoyi a ƙarshen tafsirin a inda wani ya bayar da hujjar Masallacin na karɓar kudi don kula da shi ne da kuma sayen Man dizel.

Sai Malam ya amsa da cewa hakan bai halarta ba.

“Sai dai in wasu ɗakuna aka ware a cikin masallacin wanda mutum zai kama ya zauna don yin Ibada wanda hakan ya halarta ko kuma kuɗin da ake biya na amfani da banɗakuna ne da za a shiga don biyan buƙata wanda da su za a kula da tsafta da gyaransa da kuma ma’aikata.

“Amma in don a shiga cikin Masallacin a yi Ibada ne kamar Itikafi ne sai an biya saboda a taƙaita yawan mutane, wannan bai halarta ba.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

“Wanda kuma dole ne musulmai su haɗu su yaƙi wannan bida’a wacce ta fi duk wata bida’a da wasunsu ke ta suka muni saboda abin da hakan zai haifar a nan gaba,” in ji shi.

Jaridar Aminiya ce ta ba da rahotan Masallacin Juma’a na unguwar masu hannu da shuni na Lekki da ke Jihar Legas ya saka Naira 130,000 ga duk mai son yin Itikafi a cikinsa wanda hakan ya haifar da cece-ku-ce.

Kodayake, wannan ba sabon abu ba ne a jihar a cewar wani mazaunin garin kasancewar masallatai daban-daban na karɓar kuɗi kama daga Naira 10,000 zuwa 30,000.

Sai dai rahoton da aka samu dangane da kuɗin da Masallacin Lekki ya karɓa a wannan shekara ya zarce na kowa a jihar, lamarin da ya ja hankalny jama’a a ciki da wajen jihar.

Continue Reading

Addini

Yadda azumin Ramadan ke taimakawa wajen tunatarwa da ƙara kusanci da Allah da kuma iyali

Published

on

Watan tara na Hijira a kalandar Musulunci wanda asalinsa ke nuna tarihin yadda Annabi Muhammad (S.W.A) ya yi ƙaura daga Makka zuwa Madina, a lokacin ne al’ummar Musulmai sama da biliyan 2.5 a faɗin duniya suke azumi a watan Ramadan.

Ana gudanar da azumin ne har tsawon ranakun watan baki daya tun daga ketowar alfijir zuwa faduwar rana tare da addu’o’i da kuma tunatarwa Kamar yadda koyarwar Annabi (S.A.A.W) ya bayyana.

Watan Ramadan ba wai kawai yana ƙara wa muminai ayyukan ibada da kuma tunarwa ba ne, falalal cikin wata mai alfarma yana ciyar da gangan jiki da tunani gwargwadon yadda yake tsarkake ruhi.

Lokaci ne na musamman na kamewa da kuma yin ibada da mubaya’a da ya hada biki na ibada da kuma iyali, da al’umma a lokaci guda.

Azumin Watan Ramadan

A cewar Alƙur’ani mai tsarki, azumi wani nau’i ne na ibada da aka wajabtawa dukkan muminai.

“Ya ku waɗanda kuka yi imani, an wajabta azumi a kanku, kamar yadda aka wajabta wa waɗanda suka gabace ku, saboda ku zama tsarkarku,” a cewar wata aya daga Suratul al-Baqarah a cikin Alƙur’ani.

A cewar malaman addinin Musulunci, azumi wajibi ne a watan Ramadan kuma yana da fa’idodi da falala masu yawa ga kowane mutum.

”Wannan ne watan da mutane za su nemi gafarar Allah a kan kurakuran da suka aikata, sannan suna amfani da wannan damar wajen kyautatawa iyalansu da abokansu da kuma al’ummar da suke rayuwa a cikinta,” kamar yadda malamin addinin Islama da ke Nairobi Sheikh Shaaban Ismail ya shaida wa TRT Hausa

“Duk musulmin da ya kai shekarun balaga ko sama da haka, ban da wasu ƴan tsiraru, wajibi ne su yi azumi.”

Shika-shikan Musulunci

Azumin watan Ramadan na ɗaya daga shika-shikan Musulunci guda biyar, waɗanda wajibi ne ga dukkan Musulmai su yi riƙo da su.

Na farko shi ne “shahada”, ko kuma kalmar imani da cewa Allah shi ne abin bautawa shi kadai, kuma Annabi Muhammadu manzonsa ne.

Na biyu shi ne tsayar da salloli biyar a rana sai kuma Azumi a watan Ramadan da bayar da “zakka” (aikin ba da sadaka), da kuma ziyarar Makka don yin aikin Hajjin ga wadanda suke da halin zuwa.

Iyaye Musulmai gaba ɗaya sukan koyar da ƴaƴansu tun suna ƙanana ɗaukar azumin watan Ramadan a matsayin umarni daga Ubangiji, da nufin amfanar da su ta hanyar wadatar da kowane fanni na rayuwarsu.

“Wasu daga cikin wadanda azumin bai wajaba a kansu ba sune tsoffi da marasa karfi da suka hada da masu fama da lalurar ajali, a maimakon haka ana bukatar su ciyar da miskini abinci duk ranar wata,” in ji Sheikh Shaaban.

“Idan mutum yana fama da wata rashin lafiya na ɗan wani lokaci ko kuma ya kasance matafiyi ko kuma mai ciki ko mai shayarwa, ko mai jinin haila, an kebe masu irin wannan lalura daga yin azumi, tare da gargadi kan cewa sai mutum ya rama ta hanyar sake yin azumin daga baya”.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe gomman Falasɗinawa a ranar farko ta Azumin Ramadana

Faɗaɗa ayyuka

Azumin Ramadan ba wai kawai kaurace wa ci da sha ba ne. Dole muminai su ƙaurace wa sha’awarsu kamar yin jima’i. Ana kuma buƙatar musulmi su kara taimakawa marasa karfi a cikin watan.

A bayyane yake cewa a tsawon shekaru har wasu da ba musulmai ba sun yarda tare da shaida muhimmancin watan Ramadan.

A faɗin duniya baki ɗaya, wasu waɗanda ba musulmi ba su kan yi azumi a cikin watan Ramadana mai tsarki- wasu don samun biyan bukatu na ruhinsu da kuma keɓe kawunansu don tarbiyyar da ke tattare da watan, wasu kuma don su ji yanayin da ake ji, wasu kuma a matsayin sadaukarwa ga mutanen da ke kusa da su.

“Ana so Musulmai su nisanci duk wani aiki na zunubi ko kuma na rashin ɗa’a a kowane lokaci, sannan a cikin wannan wata ana bukatar su faɗaɗa ayyukansu na alkhairi da kuma gujewa duk wata shagala ko wacce iri ce.

“Idan aka kiyaye, hakan zai kawo zaman lafiya da wadata a cikin al’umma gaba daya,” a cewar Sheikh Shaaban.

Al’adar buda Iftar, ko buɗa baki bayan faɗuwar rana a kowace rana, wani ɓangare ne na watan Ramadan wanda ya zarce iya addini kawai.

A mafi yawan lokuta, mutane kan gayyaci ’yan uwa da makwabta da abokan arziki domin su buda baki tare ta hanyar cin nau’in abinci irin daban-daban gami har ma wasu na musamman da ake ci a lokacin Ramadan.

Don haka, lokacin buɗa baki ba wai dabi’a ce ta buɗa baki kawai ba, hanya ce ta haɗa kai da kuma ƙara ɗankon soyayya da kautatawa a tsakanin al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like