Connect with us

A Gani Na

Yadda yajin aikin ASUU ya chanja min tunanina, daga Abubakar M Taheer

Published

on

Tun bayan Tsunduma yajin aiki da malaman jami’o’i sukayi kimanin watannin Uku da suka shude,
Na fara tunanin Wata hanya ce zan bi domin ribatar wannan lokaci na zaman gida.

Ni Dalibine dake ajin Karshen A Jami’a (500L) wannan tasa nayi dogon nazarin sanarwar kaina mafita da kuma tunkarar rayuwa gaba gaɗi.

Mahaifina ya daukin zunzurutun kudin makaranta ya bani domin biyan kudin karatu.

Na duba ga kudi ga yajin aiki, dayake ina Sana’ar dogaro da kaina ta Chajin Waya A garinmu.

Haka tasa Na haɗa da kudin makaranta da ɗan wanda nake samu a kasuwa na Karbi hayar gona domin noman shinkafa yar rani.

Kamar wasa na tanaji komai da ake bukata nama biya kudin hayar gona Naira dubu ashirin na dukufa nake zuwa gona kamar da Take ka fatata ta chanja zuwa baka saboda wahala.

‘Yan watanni kafinnan, munyi magana da Aunty na Dake Abuja, wanda Take Digirin digirgir ta bani shawarar daukan hanya mai ɓullewa domin samun cigaba rayuwa wannan tasa nake jin kamar anamin allurar soja wajen zuwa gona.

A haka nake shiga cikin mutanen kauye muke Caƙuduwa dasu muna idan naje Ban ruwa inayi ina ciran ciyawa.

Haka suke gwada min Rike Sprayer domin fisarar maganin kwari, Kamar Perfect Killer da Sauransu.

Idan ban sanar da kai cewa nasan Kalamar turanci daya ba, bazaka taba iya ganewa ba saboda irin kokarin danake wajen yin aiki.

A yanzu Noman shinkafa musamman ‘yar rani yana da kashe kudi kama daga Man fetur wanda duk bayan kwana biyu ko uku nakan siyi na dubu biyu zuwa sama.

Ga kuma uwa uba taki wanda nasiya daga ragowar kudin s makaranta da maigidanmu ya bani duk kudin ya tafi a yin Harrow,jiko,dashe dss.

Shagon chaji kar Dan uwansa Dalibin jami’a ya dauka a rufe yake, a’a akwai yaron da yake tattara mana taro da kwabo wanda duk wanda ya sani ya san karamar sana’a ce samun ta baikai ya kawo ba.

Abinda aka ɗan samu shine za’a siyi mai da kuma biyan kudin masu ciran ciyawa dadai sauransu. A haka aka kwashe watanni ana turawa, shinkafa ‘Yar rani Wata uku takeyi kwana casa’in, daga nan Saide kaji ana Zancen dubu daruruwan.

Misali Idan ka samu buhu Ashirin, yanzu haka ana saida kowanne dubu goma sha takwas kaga (18,000*20)=N360,000

Idan kuma ka samu sama da haka kaga kudin ya tafi.

Yanzu haka ‘yan kwanaki ya rage A bugeta a kwashe Riga a kuma cire uwar kudin.

Duk kuma a wannan lokacin daga fara yajin aikin ASUU zuwa Yau.

Shawara gareka abokina dalibin jami’a Yanzu damana ta sauka Ruwan sama ya samu kayiwa kanka karatun tanutsu, Ka nemi gona koda ta tudu ce(Gero,dawa, masara) ka noma kaine da riba.

Idan kuma yankinku da ruwa ana noman shinkafa ka Nemi gonar shinkafa ka noma .

Ana samun Miliyoyin kudi a noman Shinkafa dana Tudu a wannan zamani.

Kaine da riba, idan ASUU sun dawo Masha Allah idan basu dawo ba kaga kasami abinda Bature yake cewa Plan-B na gina rayuwarka.

Lokacin da ASUU zasu dawo Saide kaji kana Lissafin Miliyoyin a hannunka kaga Kana gama karatu Ka samu Hanyar dogaro dakai har wani ma yaci a ƙasanka.

Kaida kake da burin Gina rayuwarka kada ka bata lokacinka, Ka sani lokaci tamkar takwabine na yaki idan baka yi amfani dashi wajen yaƙi ba shi zai yake ka.

Ka sani Cewa” Time waits for no one,Time Stops for no one, your Excuses will not slow down time,Your Indecisions will not delay Time,Your Complaining will not stall time,Your regrets will not turn back Time”.

Na Barka lafiya Dan uwana dalibin Jami’a.

Aluta Kwantiniyo!!! Victoria Asata!!!.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

A Gani Na

Burina a tuna dani a marabucin da ke nusar da shugabannin – Hassan Gimba burin a tuna ni a marubucin dake nusar da shugabanni – Gimba

Published

on

“Tun Ina aji ukun firamare na ke karanta wa mutane litattafan Hausa”

Dr. Hassan Gimba ƙwararren ɗan jarida ne da ya shafe shekaru sama da 30 yana aikin jarida. Ɗan asalin garin Potiskum dake Jihar yobe, sannan mamallakin kamfanin jaridun Neptune Prime. A cikin wannan tattaunawar da ya yi da wakilinmu Abubakar M. Taheer, ya kawo irin nasarorin da ya samu a cikin aikin dama irin matsalolin da aikin na jarida yake fuskanta a yanzu. A sha karatu lafiya:

MANHAJA: Da farko za mu so ka gabatar mana da kanka ga masu karatunmu.

DAKTA HASSAN: Assalamu alaikum warahamatullah. Ni dai sunana Hassan Gimba haifaffen garin Potiskum dake Jihar yobe.
Tun tasowa Ina da sha’awar karance-karance tun Ina aji uku na firamare. Zan iya tunawa ‘yan’uwana da ƙannena sukan zagaye ni, Ina karanta musu littafin ‘Magana Jari’, ‘Ruwan Bagaja’ da Iliya Ɗan mai Ƙarfi’. A zamanin babu television sai dai a kunna fitilar ƙwai Ina karanto musu suna saurara.

Bayan nan dana shiga aji huɗu da biyar na firamare Ina karanta jarida, da yake mahaifinmu ɗan boko ne yakan dawo gida da jaridu kamar kowanne ɗan boko kan yi, jaridu kamar ‘Time magazine’, ‘Readers Digest’ da dai sauran su. Ni kullum yana dawowa na kan karɓa ne na karanta.
Nakan karanta jaridun daga bango zuwa bango nake karantawa. Da na shiga aji shida na kan siyi jaridun da kaina. A lokacin Idan zan tafi makaranta akan bani Sile goma, su kuma jaridun ana siyar su Sile ɗaiɗai ne.
A haka sai na siyi jaridun guda goma kala-kala Ina tahowa da su, Ina karantawa. A haka dai har ya zama na koyi karanta jarida dama na iya Turanci sosai.

Waɗanne ƙalubalai za a ce ka fuskanta ganin irin daɗewar da ka yi kana aikin na jarida?

To kasan ƙalubale kala-kala ne, kusan zan iya cewa kowa da yadda yake kallo ƙalubalai. Misali yawanci ‘yan jarida akwai fama da rashin kuɗi, wato rashin albashi don haka mutum yana ganin labari mai kyau don rashin kuɗi sai ya zama ba shi da
damar zuwa ya ɗauko ba. Wani lokacin ka fita daga gida ba abinci baka da kuɗin komowa gida a haka sai ya zama mutum ya kasa ɗaukan labari. Haka kuma ada za ka rubuta labari ka ɗora a mota akai hedkwatarku, amma a yanzu za ka ga ana amfani da na’urori na zamani wanda rashin su kan hana ‘yan jaridu gudanar da aikinsu.

Da yawa daga cikin matasa suna son cimma nasara a rayuwa cikin ƙanƙanin lokaci,don haka suna kallo irinku a matsayi makwafi. Ko ya abin yake?
To a gaskiya ita rayuwa babu wani abu da ake samun sa a sama, sai anyi aiki. Yawanci waɗanda suke kallo ko suke son cimma nasara cikin ƙanƙanin lokaci suna da ƙaranci ilimin zamantakewa. Ko ɗan sarki ne baya samun sarauta sai ya yi aiki tuƙuru. Da farko sai ya koyi ilimin zama da mutane, girmama manya da kuma sanin ilimin shugabantar jama’a. Wannan ne zai ba shi dama mutane su ga ya kamata su zaɓe shi.

Duk wanda ya fara wani abu daga sama, to ba zai jima ba zai ruguje. ko kuɗi ne, sai mutum ya fara da yaron shago, kwana a ɗaki ɗaya har Allah ya yi ya zama hamshaƙin mai kuɗi. Idan malinta ce sai ka fara da ƙolonta har zuwa farfesa.
Haka shima a aikin na jarida dole za ka fara da bin manya kana koya har ya zama ka iya. Misali ka ɗauka ni, yanzu haka Ina da shekaru kusan 31 a aikin jarida.

Nasarori fa za mu su mu ji waɗanne ka samu?

To alhamdu lillah. Kasan ita nasara kowa da abinda yake kallo a matsayin nasara. Ni ta nawa janibin ta wannan aikin na yi aure na hayayyafa a aikin nake ciyar da kaina da iyayena da iyalaina dama tallafa wa marasa ƙarfi. Kuma iya gwargwado Ina gode wa Allah kan hakan.
Bayan aikin jarida kenan kana da wata gidauniya ta tallafa wa marasa ƙarfi?

Eh, alhamdu lillah, zan ce Ina da gidauniya guda biyu ta taimaka wa al’umma. Na farko Ina da gidauniya mai sunan matata wanda ta rasu sanadiyyar sanƙarar mahaifa shekaru huɗu da suka wuce, wanda muke tallafa wa masu fama da wannan cutar da ba su magani ajin farko tare da wayar musu da kai kan haɗarin cutar.

Akwai rubuce-rubuce da nake yi a jaridar Blueprint da NewNigeria da wasu jaridun ‘online’ sun kai tamanin da wani abu inda muka tattara shi rubutun ya zama littafi guda biyu. Aka ƙaddamar da su, kuɗin da aka samu yanzu haka mun fara gina asibitin masu fama da cutar kansar mahaifa.
Haka kuma Ina da gidauniya da na buɗe mai sunan Abokina Ɗan Jarida Abubakar Monja wanda muke tallafa wa iyalan ‘yan jaridun da suka rasa ransu sanadiyyar harin Boko Haram da sauran haɗarori.

A shekarar 2007 Dakta ya fara shiga harkar siyasa. Shin aikin jarida ne ya kaika wannan matsayin ko yaya lamarin ya kasance?

Eh abinda zan ce shine, a shekarar 2007 na shiga harkar siyasa gadan-gadan a lokacin da wani aminina Tijjani Musa ya yi gwamna a Yobe, ya nemi na taimaka masa inda na fito takarar sanata a Jam’iyyar AC.
Bayan wannan kuma ina ga ban sake shiga harkar siyasa ba sai dai na marawa ‘yan siyasa baya waɗanda za su tallafa wa al’umma, Ina nufi ni nakan bi mutum ne ba jam’iyyar.

A ‘yan shekarun baya- bayan nan, ka buɗe kamfanin jaridarka na ‘Neptune Prime’ da ke yaɗa labarai da ‘online’. Waɗanne nasarori za a ce an samu daga buɗewa zuwa yanzu?

To alhamdu lillah. zan iya cewa, bayan na zama ‘reporter’ a jaridu da dama kamar ‘Today Newspaper’, ‘Daily monitor’, ‘This day’ da sauran su, sai na koma gida Potiskum na yi wata jarida Informant muka samu shekaru.

Daga nan sai na koma Abuja muke buga ‘Pen Watch’ a 2008 a lokacin muna bugawa tare da ‘Leadership’ a kamfani ɗaya.Daga nan sai na dawo ‘Leadership’ na zama edita nata, bayan zama edita daga nan minister na ‘Science and Technology’ a shekarar 2004 ya neme ni na zame masa S.A kan ‘Media and Publication’.

Daga nan na sake dawo wa Leadership Friday na zama editan inda na bar su a shekarar 2016. A shekarar 2017 a April sai na buɗe kamfanina na ‘Neptune Prime’ wanda muke watsa labarai online. Inda a bara na buɗe Neptune Prime Magazine, bana kuma muka fara talabijin na Neptune Prime.
Waɗanne abubuwa ka ke so ace al’umma ta tuna da kai da shi a matsayinka na tsohon ɗan jarida?

To alhamdu lillah, zan iya cewa kusan kowa za ka ga yana da abinda yake so ace bayan rayuwarsa an tuna da shi haka nima. Ina fatan ace wannan kamfanoni nawa na jarida ace ko bayan raina su ci gaba da gudana domin jama’a su tunani a matsayin marubuci wanda yake rubutu kan rayuwar ɗan adam da nusar da shuwagabanni yadda ya kamata su jagoranci al’ummarsu.
Wane kira ka ke da shi ga matasan ‘yan jarida da ma matasa bakiɗaya kan cimma nasara a rayuwa?

To alhamdu lillah, kira na da nake da shi ga matasa shine, su zamanto masu haƙuri. Kusan al’adar matashi shine rashin haƙuri, kusan idan ya ga wani babba yana da burin ace ya cimma sa.

Ba a samun haka sai anyi haƙuri an kuma yi aiki tuƙuru yau da gobe ana samun shekaru har Allah Ya kai ka kan wannan matsayin.

Idan ka duba za ka ga wani ya ɗauki shekaru20, 30 waje cimma nasararsa, amma matashi kullum ya rinqa tashi da jin cewa, yana son yin daidai wannan. Haƙuri da jajircewa na taimaka wa wajen cimma nasara a rayuwa.

Aikin jarida yana fuskantar barazana sakamakon bayyanar kafafen sada zumunta. Wane kira ka ke da shi musamman ga ‘yan jarida kan aikinsu?

To a yanzu gaskiya sakamakon bayyanar kafafen sada zumunta da mutum ya samu data shima ya zama ɗan jarida. Wanda kuma lallai ba haka abin yake ba, aikin jarida aiki ne da yake da tsari yake da manufofi ba kamar na sada zumunta ba.
To dole ɗan jarida ya zama yana kan wannan tsari domin ya bambanta da ɗan ‘social media’. Ya zama yana rubutu domin ƙaruwar al’ummarsa da ma duniya bakiɗaya.

Continue Reading

A Gani Na

Meye ra’ayinka kan mauludi? Tattaunawarmu da wani a kan Mauludi, Daga Yusuf Alhaji Lawan

Published

on

Na fito da safe zan raka yara makarantar Islamiyya a wata ranar Asabar, isar mu bakin makarantar ke da wuya, sai ga abokina shima ya kawo nasa yaran. Bayan sun shiga sai ni dashi muka kamo hanyar komawa gidajenmu.

To wannan ranar tayi dai-dai da 12 ga watan Rabi’ul Auwal. Sai muka ci karo da yara ‘yan Islamiyyoyi da kayan makaranta wasu da shiga kala-kala zasu tafi wajen zagayen Mauludi. Cikin wasa sai nacewa abokina, kaga muma da munyi sabbin dinki iri ɗaya ai da munje riyadar mauludin nan, yace gaskiya fa.

Da muka cigaba da tafiya, sai yace mun wane, mu ajiye maganar wasa a gefe, don Allah meye ra’ayinka a kan mauludi? Sai na kada baki nace masa ai ni bani da matsala da mauludi. Sai yace mun to shi yana da matsala da mauludi. Nace masa to ina sauraronka. Sai ya ƙara da cewa akwai Hadisin Annabi da yace duk wadda ya ƙirkiro wani abu a cikin addini to ba’a karba ba. Da wannan dalilin ne yasa shi baya tare da mauludi.

Nace masa to wane ni yanzu ba zan baka wata hujja ta yin mauludi ba, amma zan faɗa maka wasu abubuwa irin mauludi da suma aka ƙirkiro su da zaka taya ni neman hujjojinsu. Idan ka samo, to sai mu dawo kan mauludi. Yace mun yana saurarena.

Ban san ko ka taba halartar tafsirin Al-Qur’ani mai Girma a cikin watan Ramadana ba. Yace sosai yana halarta. Nace masa to a Makka ko Madina Annabi ya fara tafsirin Al-Qur’ani a Ramadan? A shekara ta nawa kafin hijira ko bayan hijira ya fara? Cikin sahabbai waye mai ja masa baki? Bayan Sallar Asuba yake yi ko da hantsi? Da yamma ko da dare? Maza da mata yake yiwa a hade ko kowa daban yake musu nasu? Idan yayi fashin fitowa waye yake gabatarwa a madadinsa?

Sai gasar karatun Al-Qur’ani. Ita kuma a wace shekara Annabi ya fara shiryawa? Cikin sahabbai waye yake zama zakara? Wadanne kyaututtuka yake rabawa ga wadanda suka yi fice? Ruwayoyin Qira’a nawa aka yi amfani dasu? Su waye manyan alƙalan gasar?

Sanya sunayen sahabbai ko wasu bayin Allah na gari ga masallatai. Shi Annabi wane suna ya sanyawa nasa masallacin? Sannan a tarihin rayuwarsa masallatai nawa ya sawa suna? Sannan menene misalsalai na irin sunayen da yayi ta sakawa masallatai?

Sallar Tahajjud jam’i a masallatai da azumi. Ruwayoyi nawa aka samu da suka zo da yadda Annabi yake gudanar da sallar Tahajjud jam’i a masallacinsa? A wace shekara ya fara? Da kira’ar Hafsi, Warshi, Tangimi, Duri ko Susi yake karatu? Sannan kowace raka’a sumuni ko rubu’i ko izu yake karantawa? Sannan saukar Qur’ani yake yi cikekke ko wasu izu yake karantawa? Idan akwai ranar da bai samu fitowa ba, cikin sahabbai waye yake gabatarwa a madadinsa? Shi kadai yake yin limancin ko suna yin karba-karba da wani ko wasu daga sahabbai?

Sallar Tarawihi jam’i a masallatai. Malamai sun faɗa mana cewa tunda Annabi yayi sau 2 a masallaci mutane suka bishi bai sake yi ba, yace ina tsoron a wajabta muku kuma ba zaku iya ba, sai ya koma gida yana yi shi kadai, kuma har ya bar duniya ba’a kara yin sallar Tarawihi jam’i a masallacin Annabi ba. Har Sayyidina Abubakar ya gama halifancinsa ba’a yi Tarawihi jam’i ba. To da wane dalili aka jingina yanzu ake yin sallar Tarawihi jam’i a masallatai?

Kafa kwamitin masallaci kuma sunnar waye? A zamanin Annabi waye ciyaman din masallacin Annabi? Waye ma’aji? Waye magatakarda? Waye jami’in hulda da jama’a na masallacin Annabi?

To wa’azin ƙasa fa? Wa’azin jiha dana karamar hukuma? Idan Annabi ne yayi, to a shekarar daya fara su nawa ne suka gabatar da muhadara a wajen? Alarammomi nawa ne masu jan baki ga Malamai da suka gabatar? A wane gari Annabi ya fara?

To dama wasu ire-iren waɗannan da lokaci ba zai bani damar gama kirga maka su ba, ina son ka taya ni nemo hujjojinsu a Qur’ani ko Hadisan Annabi. Idan ka samu to sai nima na nemo maka hujjar mauludi.

To amma ina mai tabbatar maka cewa zaka sha wahalar nema kuma da wahala ka iya samo hujja ta kai tsaye akan duk waɗannan tambayoyi sai dai tawili. To kuma duk wata hujja da zaka samar ta tawili to mai mauludi ma zai hau kai. Idan kace ana yin gasar karatun Al-Qur’ani ne saboda a sanya son Qur’ani a zuƙatan musulmi ko don a ƙarfafa koyonsa, mai mauludi ma zai ce maka ai wannan shine dalilin mauludi kuma shi yasa ake karatun Al-Qur’ani a wajen. Idan kace sanya sunan sahabbai ko bayin Allah na gari a masallatai aikin kirki ne, to mai mauludi ma zai ce maka shima Mauludi aikin kirki ne da kuma sauran dalilai irin wadannan.

Idan ka gamsu cewa yin tafsirin Al-Qur’ani a Ramadan, Sallar Tahajjud jam’i, Gasar karatun Al-Qur’ani da sauransu duk basu da hujja ta kai tsaye daga Annabi to amma kai sun maka, kuma zaka yi su, to sai ka yarda cewa yadda kake da ‘yancin yin su, haka mai yin mauludi ma yana da irin wannan ‘yancin.

Idan kuma ba haka ba, to sai mu hada kai mu watsar da dukkan wadannan abubuwan har ma da wadanda ban ambata ba tunda Annabi bai yi su ba.

Sai abokina yayi shiru na wani ɗan lokaci sai yace mun to yaya aka yi malaminsu bai san duk wadannan bayanan da nayi ba? Nace masa ya sani mana, kawai ba zai fada muku bane tunda shi yana da tasa manufar. Sai yace mun wallahi malaminsu bai san duk wadannan ba kuma sai yaje ya same shi ya fada masa.

Bayan mun gama tattaunawa, sai muka rabu kowa ya wuce gida. To yanzu ina saurare naga ko zai dawo ya fada mun yadda suka yi da Malaminsa ko a’a. Zai sassauta ya daina fada da mauludi ko zai fara yin mauludi shima. Zai kaikasa kasa ya cigaba da sukar mauludin ko zai yi shiru.

Allah ya ƙara mana soyayyar Ma’aiki s.a.w, ya sanya mu cikin cetonsa. Allah ya haskaka zuƙatan musulmi su fahimci daɗin soyayyar Annabi Muhammadu s.a.w.

Continue Reading

A Gani Na

Ƙarancin ma’aikatan tsaro, makaman yaƙi na zamani, rashin horaswa ne matsalar murƙushe ta’a’ddanci a Nijeriya, daga Dahiru Suleiman Dutse

Published

on

Wani masanin harkokin tsaron ƙasar nan, Dokta Yahuza Getso (Mai ritaya), ya lura da cewa ƙarancin maaikatan tsaron ƙasa, da ƙin ba sojoji makaman da ya dace, da rashin tura su kwasa- kwasan Sanin makamar yaki da tinkarar abokanen gaba ne ummul haba’i’sin kasa shawo Kan matsalar tsaro a Nijeriya.

Dokta Getso na faɗin hakan ne a tattaunawarsu da wakilinmu a garin Dutse, inda ya nuna takaicinsa da yawaitar ayyukan taddanci babu ƙaƙƙautawa, inda ya dora alhakin hakan a kan sakacin mahukunta, a sabili da rashin gaskiya da adalci.

Ya ƙara da cewa, “da akwai ban takaici ganin yadda ba mu da wadatattun sojoji a ƙasar nan da za su iya murƙushe ayyukan taddanci cikin ƙanƙanin lokaci a sabili da kwadayi, zalunci, da son zuciyar wadanda alhakin kula da wannan bangaren ya rataya a wuyansu.

“Adadin sojoji da ‘yan sandanmu ba su gaza fiye da mutum dubu hamsin ba, ga shi Kuma an ƙi ba su makaman da ya dace a ba su a sabili da munafunci, cin hanci da rashawa, gami da son zuciya, to ta yaya za su iya tinkarar abokanen gabansu, wadanda ke dauke da muggan makamai, ga su Kuma da gogewar Sanin makamar yaki” in ji Dokta Getso.

Saboda haka acewarsa, “hanya ta farko da za ta wanzar da maslaha ga wannan ta’addanci ita ce, lallai mahukunta su ba da amincewar ƙarin daukar ma’aikata aikin soja, da na ‘yan sanda, da makamantansu. Ba ya ga haka, a rika ba sojojinmu makaman da ya dace, kuma irin na zamani, tare da ba su horo kan sanin sabbin dabarun yaƙi da fuskantar abokanen gaba akai akai.

“Ya zama wajibi mu ƙara ba sojojinmu kulawa ta sosai, musamman abin da ya danganci wadata su da isasshen kayan aiki, da kyakkyawan albashi, da yanayin wurin zama, ma’ana muhalli mai kyau.

“Muddin ba wadannan matakai muka runguma ka’i’n da naim ba, babu ta yadda za mu yi adabo da matsalar tsaro a Kasar nan”.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like