Connect with us

Kasashen Waje

Yadda Sarkin Farisa ya yanke hukuncin feɗe fatar alƙali da ransa

Published

on

Wannan wani zane na karni na 16, dake nuna fatar jikin wani alƙali da yayi rashin daraja, me suna Sisamnes, a shekara ta 500BC.

Sisamnes ya kasance alƙali mai cin hanci da rashawa a lokacin Cambyses ll a Farisa. An gano cewa ya karbi cin hanci a kotu kuma ya yanke hukuncin da bai dace ba.

Saboda haka ne sarki ya ba da umarnin a kama shi da laifin cin hanci da rashawar, sannan ya ba da umarnin a yanke fatarsa da ransa kafin a kashesa, domin yaji raɗaɗin cirewar.

Kafin yanke hukuncin, sarki ya tambayi Sisamnes wanda yake so ya nada a matsayin magajinsa. Sisamnes, a cikin son kansa, ya zaɓi ɗansa, Otanes. Sarki ya yarda, kuma ya nada Otanes ya maye gurbin mahaifinsa.

Bayan an zartar da hukuncin, Sarkin ya kuma ba da umarnin a yi amfani da fatar Sisamnes da aka cire, don lulluɓe kujerar da sabon alkali zai zauna a kotu. Yayi hakan ne domin tunatar da shi illar cin hanci da rashawa.

Wannan yasa dole Otanes, ya dinga tunawa a koyaushe, yana zaune a kan fatar mahaifinsa da aka kashe. Wannan ya taimaka wajen tabbatar da adalci da daidaito a cikin dukkan sauraren ƙararsa, shawarwarinsa da hukunce-hukuncensa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra’ila

Published

on

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra'ila

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra’ila

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ke ƙare yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.

Manyan ‘yan takarar shugabancin Amurka biyu, mataimakiyar shugaban ƙasa Kamala Harris da tsohon shugaban ƙasa Donald Trump, sun ya yi Allah-wadai da zanga-zangar nuna adawa da Isra’ila wacce aka fara ranar Laraba a kusa da ginin majalisar dokokin Amurka.

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ke kare yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.

Harris, wacce ta yiwu ita ce ‘yar takarar shugaban ƙasa ta jam’iyyar Democrat a zaɓen shekarar nan ta 2024, a cikin wata Sanarwa ta ce “Mun ga ayyukan Allah-wadai daga marasa kishin ƙasa masu zanga-zanga da munanan kalaman ƙiyayya a tashar jirgin ƙasa ta Union Station da ke kusa da ginin majalisar dokoki.”

KU KUMA KARANTA:Joe Biden ya janye daga takarar shugaban Amurka

A gaban tashar, masu zanga-zangar sun cire tutocin Amurka suka sanya Tutocin Falasɗinawa, sannan wani mutum ya yi amfani da jan fenti ya rubuta “Hamas na nan tafe” da manyan harrufa a kan wani babban sassaƙe. Bayan haka Masu zanga-zangar sun ƙona wani mutum-mutumi na Netanyahu da tutar Amurka.

Shi ma Trump, ya rubuta a shafin sa na sada zumunta na Truth cewa “Idan da waɗanda suka ta da tarzoma jiya a Washington ‘yan Republican ne, da yanzu dukkansu na tsare a gidan yari, suna fuskantar hukuncin ɗauri na shekaru 10 zuwa 20. Amma a ƙarƙashin wannan Gwamnatin, babu abin da zai same su.”

A jiya Alhamis Shugaban Amurka Joe Biden ya karɓi baƙuncin Firai Minista Benjamin Netanyahu a fadar White House, don tattaunawa da nufin ganin an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kuma sakin sauran mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su, tun bayan harin da ta kai kan Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoban bara.

Shugabannin biyu sun gana a Ofishin shugaban kasa, kwana daya bayan da dukkansu sun gabatar da muhimman jawabai. A ranar Laraba Netanyahu ya yi magana a gaban Majalisar Dokokin Amurka, inda ya kare yaƙin da ƙasarsa ke yi da mayaƙan Hamas.

Shi kuwa shugaba Biden ya yi jawabi game da dalilin da ya sa ya yanke shawarar janyewa daga takarar shugaban ƙasa a ranar Lahadin da ta gabata, tare da bayyana goyon bayansa ga mataimakiyarsa.

 

Dukkan shugabannin biyu sun gabatar muhimman jawabai a taƙaice kafin ganawar da suka yi ta sirri.

To sai dai gabanin ganawar, wani babban jami’in gwamnatin ƙasar ya shaidawa manema labarai cewa shugabannin biyun suna aiki kan cikakkun bayanai game da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma sakin waɗanda aka yi garkuwa da su, “wadda suka ce sun yi imani ana a matakin ƙarshe.”

Continue Reading

Kasashen Waje

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

Published

on

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

An kashe aƙalla mutane 13 a wasu hare-hare uku da Isra’ila ta kai kan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke tsakiyar Gaza cikin daren Juma’a zuwa jiya Asabar, a cewar jami’an kiwon lafiyar Falasɗinu, yayin da ake ganin ana samun ci gaba a tattaunawar tsagaita buɗe wuta a birnin Alkahira.

Daga cikin waɗanda suka mutu a sansanin ‘yan gudun hijiran Nuseirat da kuma sansanin ‘yan gudun hijiran Bureij, akwai yara uku da mace guda, a cewar ƙungiyoyin agajin gaggawa na Falasɗinawa da suka kai gawarwakin zuwa asibitin Al-Aqsa Martyrs da ke kusa. ‘Yan jaridan AP sun kirga gawarwakin mutane 13 a asibitin.

Mace macen baya-bayan nan na zuwa ne adaidai wani lokaci da ake bege gani a yakin da ya addabi Gaza, bayan da tawagar likitocin suka ceto jariri da rai daga wata mace Bafalasdina mai juna biyu da aka kashe a harin na jirgin sama da ya fada kan gidanta da ke Nuseirat da yammacin ranar Alhamis.

An kashe Ola al-Kurd mai tsohon ciki mai shekaru 25 tare da wasu mutane 6 a tashin bam ɗin, amma jami’an agajin gaggawa suka garzaya da su asibitin Al-Awda da ke arewacin Gaza da fatan ceto yaron da ke cikinta. Sa’o’i kaɗan bayan haka, likitoci sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa an haifi yaron.

Jaririn da har yanzu ba a raɗa masa suna ba yana cikin koshin lafiya, sai dai yana fama da ƙarancin iskar oxygen kuma an sanya shi a cikin na’urar incubator, in ji Dr. Khalil Dajran. Mahaifin yaron ya samu rauni a wannan harin, amma ya tsira da ransa.

KU KUMA KARANTA:Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 48 a Gaza a ƙasa da awa ɗaya

Yakin na Gaza, wanda ya ɓarke sanadiyar hari da Hamas ta kai wa kudancin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba, ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 38,900, a cewar ma’aikatar lafiyar yankin, wadda ba ta banbance tsakanin mayaka da fararen hula a kidayar ta.
Yakin ya haifar da bala’in jin kai a yankin Falasɗinawa da ke gabar teku, inda aka raba mafi yawan al’ummarta miliyan 2.3 da muhallansu tare da janyo yunwa mai yawa.

Harin na Hamas a watan Oktoba ya kashe mutane 1,200, galibi fararen hula, sannan mayaƙan sun yi garkuwa da kusan mutane 250.
Kimanin mutane 120 ne suka rage a hannu ake garkuwa da su, inda aka yi imanin kusan kashi uku daga cikinsu sun mutu, a cewar hukumomin Isra’ila.

Continue Reading

Kasashen Waje

Babban sakatare na jami’ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Published

on

Babban sakatare na jami'ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Babban sakatare na jami’ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Nguyen Phu Trong, babban sakatare na jam’iyyar gurguzu mai mulki a Vietnam, kuma ɗan siyasa mafi ƙarfi a ƙasar, ya rasu sakamakon rashin lafiya na tsawon watanni, kamar yadda kafafen yaɗa labarai suka faɗa a ranar Juma’a.

KU KUMA KARANTA:Jam’iyar Republican ta tsayar da Donald Trump takarar shugaban ƙasa karo na uku
Ya rasu yana da shekaru 80 a duniya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like