NNPP ta yaba wa hukuncin da kotun ƙoli ta yanke kan zaɓen gwamnan Kano

0
92

Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) ta yaba wa Kotun ƙoli bisa jajircewarta wajen tabbatar da adalci wajen tabbatar da zaɓen Gwamna Abba Yusuf a matsayin Gwamnan Jihar Kano.

Shugaban riƙo na NNPP na ƙasa, Abba Ali ne ya bayyana haka a Abuja a wani taron manema labarai.

“Muna so mu yaba da muryar mai shari’a Okoro lokacin da ya buƙaci alƙalai da su kasance masu hazaƙa a cikin ayyukansu.

“Muna so mu ƙara da cewa alƙalai su ci gaba da jajircewa da tare da sauƙe nauyin da ke kansu ba tare da fargabar alheri ba.

“Ya kamata su yi mai yiwuwa da duk wani matsin lamba na ciki dana waje kuma suyi aiki da lamirinsu. Wannan ya zama dole ga ɓangaren shari’a ya ci gaba da riƙe amana da mutuntawa a matsayin “bege na ƙarshe na talaka.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Kano ya naɗa Kwankwaso, Shekarau, da Ganduje muƙamai a Jihar

Ali ya yabawa ‘yan Najeriya, ƙasashen duniya, kafafen yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki bisa goyon bayan da suke bayarwa.

“Gwagwarmaya don ceton Kano wani yunƙuri ne na jam’iyyu da dama da suka haɗa da duk masu ƙaunar dimokuraɗiyya a faɗin ƙasarmu ta Najeriya da kuma faɗin ƙasarmu,” in ji shi.

Leave a Reply