Tinubu/Shettima: Wannan tikitin babbar nasara ce ga Jam’iyyar APC – Gwamna Buni

2
317

Gwamna Mai Mala Buni, na Jihar Yobe ya taya dan takarar shugaban ‘ƙasa na Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, murnar zabar wanda ya cancanta ya zama mataimakin shugaban ƙasa, kana ya bayyana zabin Sanata Kashim Shettima babbar nasara ce ga Jam’iyyar APC.

Gwamnan wanda shi ne tsohon shugaban kwamitin riko na Jam’iyyar APC, ya bayyana tikitin Tinubu/Shettima a matsayin tikitin nasara ga jam’iyyar. Ya ce zaben Shettima, zai wadatar da dimbin magoya baya ga Jam’iyyar da kyakkyawar damar samun nasara a babban zaben 2023.

“Haɗin kai da Tinubu da Shettima ya sa Jam’iyyar ƙarin ƙarfin tunkarar zaɓen shugaban ƙasa a shekara mai zuwa tare da samun nasara a fili” in ji shi. Gwamna Buni ya ce ‘ɗan takarar shugaban ƙasa da mataimakinsa na jam’iyyar APC, mutane ne da ke da dimbin gogewa a harkar mulki domin ganin Najeriya ta samu ci gaba.

“Kwarewarsu na gudanarwa, kwarewa da labaran nasarori sun shirya su yadda ya kamata domin shugabancin ƙasar nan.” Najeriya zata samu ɗimbin nasarori da ɗimbin riba daga gwamnatin Tinubu/Shettima idan aka zabe su a ofis” inji shi.

Gwamnan ya ba da shawarar cewa a wannan mawuyacin lokaci na taɓarɓarewar tattalin arzikin duniya, Najeriya na bukatar kyakkyawar hadin kai da gogewa irin ta Tinubu da Shettima. Ya kuma bukaci jam’iyyar da ta ci gaba da kasancewa da hadin kai tare da mai da hankali wajen samun nasara a zaben 2023.

Gwamnan Jihar Yobe ya lura cewa Tinubu da Shettima suna mutunta duk wani addini, wanda hakan ya sa
Tikitin Musulmi-Musulmi ya fi karɓuwa saboda, dukkansu suna da juriya na addini, suna aiki da zama tare da mutane daga addinai daban-daban.

Gwamna Buni ya ce “APC tana da mutane sama da miliyan 40 da yardar Allah za ta lashe zaben 2023 bisa gaskiya da adalci.

2 COMMENTS

Leave a Reply