Connect with us

Kasuwanci

Taron Bita: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci ‘Yan Najeriya Da Su Yi Rajistar Inshorar Takaful

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WASU malaman ilimi da kwararru a harkar inshora sun buƙaci ‘yan Najeriya da suka hada da ‘yan kasuwa da su yi la’akari da rungumar inshorar Takaful. Sun bayyana cewa Inshorar ya kasance mafi inganci kuma mai ɗabi’a wanda ke da fa’idodi masu yawa ga duk al’umma ba tare da la’akari da addini, ƙabila, ko matsayin zamantakewa ba.

Bayanin hakan ya fito ne a taron Takaful da kamfanin Noor Takaful Insurance Limited ta shirya a ranar Laraba, 16 ga Maris, 2022, a Jihar Kano.

Da yake gabatar da jawabinsa na maraba, Shugaban Kamfanin Noor Takaful Insurance Limited, Mista Muhtar Bakare, ya bayyana cewa taron bitar na daya daga cikin dimbin hanyoyin da kamfanin ke da niyyar jawo hankalin al’umma da kuma wayar da kan jama’a da ake bukata game da inshorar Takaful.

Ya ce “Wannan shi ne karo na farko a jerin tarurrukan da Noor Takaful ke shirin gudanarwa a garuruwa daban-daban na kasar nan, kuma ya kamata mu fara wannan tafiya a Kano. Na yi farin cikin ambaton cewa an haifi Noor Takaful a Kano a shekarar 2015.

“Wannan taron na nufin ya ba mu damar jin ta bakin malaman addinin Musulunci da na ilimi ta yadda za a san Takaful za ta taimaka wajen tallafa wa kasuwanci da al’umma kamar yadda duniya ta ke mai saurin canzawa, da kuma kalubale.

Acewar Bakare, baje kolin nasu zai ci gaba da hulda da mutane a wurare daban-daban nan da kwanaki masu zuwa.

Shi ma da yake nasa jawabin, mataimakin shugaban kamfanin, Malam Aminu Tukur, ya bayyana cewa kamfanin ya yi matukar farin cikin sake dawo da inshorar Takaful a kasuwar Kano, bayan da ya fara tafiya daga tsohon birnin.

Tukur ya ci gaba da cewa, kamfanin ya jajirce wajen inganta hada-hadar kudi ta hanyar inshorar Takaful ta hanyar samar da kayayyakin da suka dace da kowane fanni na zamantakewa.

Yayin da yake bayani kan manufofin inshorar Takaful, ya jaddada cewa tana gudanar da ayyukanta ne ta hanyar hada kudade tare domin ‘yan uwantaka.

Da yake tsokaci a wajen taron, malamin addinin Islama Dakta Bashir Umar ya bayyana cewa abin farin ciki ne ganin yadda Kamfanin ke daukar kalubalen bunkasa Takaful. Hakan ya nuna aniyar inganta inshorar da’a a Najeriya.

A cewar Umar, yanzu babu wata hujja ga musulmi musamman na yin rajistar kayayyakin inshora na yau da kullum tunda akwai kayayyakin da a yanzu suka dace da Sharia.

Shi ma da yake nasa jawabin mataimakin daraktan cibiyar bankin musulunci na kasa da kasa na Jami’ar Bayero ta Kano Dakta Warshu Rabi’u ya bayyana cewa duk da cewa inshorar Takaful tana nan daram idan aka kwatanta da inshorar da aka saba yi, masana’antar ta samu gagarumin ci gaba a kasuwannin duniya har girman ta kai Dala $22m cikin kankanin lokaci.

Rabiu ya bayyana cewa da shirin baje kolin da Noor Takaful ta fara, tana da kwarin gwiwar cewa Najeriya za ta zama jigo a masana’antar nan gaba kadan.
Ya bayyana cewa akwai bukatar ‘yan Najeriya su yi amfani da ita ganin cewa tana aiki ne bisa ka’idojin Shari’a da ke jaddada darajar taimakon juna da ‘yan uwantaka.

“Dole ne in yaba wa Noor Takaful da ta fara wannan wayar da kan Jama’a domin hakan yana taimakawa wajen sanya Najeriya cikin taswirar duniya idan ana maganar inshorar shari’a.

Ya ce biyan rarar kudi da gaggawar biyan kudaden da’awar ita ce hanya mafi girma ta shiga kasuwa”, in ji shi.

A nata jawabin, Daraktar Cibiyar Bankin Musulunci da Kudi (IIBF) ta Jami’ar Bayero ta Kano, Farfesa Binta Jibril ta bayyana cewa, babu lokacin da ya fi dacewa da za a ilimantar da ‘yan Najeriya musamman na Arewacin kasar nan kan alfanun Inshora Takaful banda yanzu domin hakan zai taimaka wajen gyara kuskuren akidar cewa kowane nau’in inshora bai sabawa Musulunci ba.

Jibril ta ci gaba da cewa, a tsawon shekarun da suka gabata, al’ummar yankin Arewa na ci gaba da nuna shakku kan batun Inshora tun da ya saba wa tsarin addinin Musulunci.

“A baya, mutane sun yi ta shakku kan batun Inshora a kan cewa ba su san abin da za a yi amfani da kudadensu ba. Talakawan Arewa na damuwa ko za a yi amfani da jarinsa ko kuma kudadensa daidai da koyarwa Alkur’ani,” inji ta

Yayin da ta yaba wa mahukuntan kamfanin kan kawo irin wadannan damammaki a Arewa, ta bukaci maza da mata da su yi amfani da damar da suke da ita ta hanyar biyan duk wasu manufofin da ake da su.

Shi ma da yake jawabi, Manajan Daraktan Noor Takaful Insurance Limited, Rilwan Sunmonu, ya shawarci ‘yan Najeriya da su shiga cikin fa’idodin ta hanyar biyan kuɗi daban-daban.

Taron mai taken: “Takaful insurance in an increasingly unstable and the unsecurity world” ya samu halartar fitattun malamai a fannin ilimi da masana’antu, wasu daga cikinsu sun hada da wani malamin addinin Islama, Dakta Bashir Umar, tsohon kwamishina a NAICOM, Malam Mohammed Kari, Darakta. International Institute of Islamic Banking and Finance, (IIIBF), Bayero University Kano, Professor Binta Jibril da dai sauransu.

Kamfanin Noor Takaful Insurance Ltd, kamfanin inshorar Takaful, NAICOM ne ta kafa ta kuma ta ba ta lasisin da ya dace a watan Afrilun 2016 a matsayin cikakken kamfanin inshorar Takaful na farko a Najeriya mai kaso 100 na hannun jarin Najeriya.

Kamfanin a halin yanzu tana taka rawar farko da kuma jagoranci wajen buɗe yuwuwar inshorar Takaful ga Najeriya. NAICOM ne ke tsara tsarin aikinsa kuma tana ƙarƙashin Dokar Inshora ta 2003.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasuwanci

Farashin kayan abinci daga kasuwar Anchau ta jihar Kaduna

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Farashin kayan abinci a jiya 23th April 2024

Masara
Me aure dubu 47 – 45 – 44
Marar aure dubu 42 – 41- 40

Farin wake
Dubu 90k 85k 80k

Waken suya
Dub 50k

Dawa
Dubu 43k 40k

Barkwano
Dubu 60k 57k

Tattasai
Busasshe dubu 70

Tumatir busasshe dubu
Dubu 70k

Tarugu
Dubu 45k 43k

KU KUMA KARANTA: Farashin kayan abinci a wasu kasuwanni a wannan makon

Shambo
Dubu 28k 27

Shinkafa me bawo
Dubu 40k 38k

Kwalin sugar mazarkwaila
Dubu 27k 26k
Karami dubu 17k 16k

Taki urea dubu 31k 30k
Indorama npk dubu 40k

Npk magic dubu 38k

Cement
Dubu 7100

Dauro
Dubu 55k 53k

Buhun fulawa
Dubu 53k

Buhun sugar
Dubu 77k

Kwalin taliya
Dubu 12,500

Indomie
Chaerie dubu 10,800
Supreme dubu 10,700

Macaroni dubu 12,500

Buhun dabino
Dubu 177k – 160k

Goriba
Dubu 13k – 12k

Kwanon rufi
Dubu 65 – 63

Abincin dabbobi

Dusa na inji menauyin 75kg Dubu 23 – 22k

Dusa tankaɗaɗɗiya menauyin 50kg dubu 14,000k

Garin Ɗorawa menauyin 65kg dubu 13k 14,500k

Kowa menauyin 35kg dubu 8k – 9k

Bincike da ƙwaƙƙwafi
Sarkin kasuwar Anchau

Continue Reading

Kasuwanci

Farashin kayan abinci a wasu kasuwanni a wannan makon

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

A kasuwar Bokkos da ke Jos, ranar Alhamis an sai da jar masara buhu ɗaya 50,000
Fara 48,000

Acca kwano ɗaya 3,200
Manya fara 3,100.

A kasuwar Mangu masara an sai da buhu ɗaya 51,000.

Haka aka sayar a kasuwar Barikin Ladi.

Kasuwar Azare jiya Lahadi.
An sayar da Dawa ja 56,000
Fara 54,000

Gero 56,000

Wake 95,000 zuwa
100,000.

Rogo busashshe 30,000 buhu ɗaya.

An sayar da buhun tsamiya 12,500.

An sayar da gyaɗa mai kwanso 30,000 buhu ɗaya.
Haka farashin ya kasance jiya a kasuwar Jama’are da kasuwar Sakuwa.
Shinkafa kuwa kwano ɗaya ‘yar ƙasa daga 3,000 ne zuwa 3,400.

KU KUMA KARANTA: Turkiyya na fatan bunƙasa kasuwanci da Saudiyya zuwa dala biliyan 30

Da muka leƙa kasuwar dabbobi kuwa an yi jugum-jugum tsakanin mai saya da mai sayarwa kowa yana kukan tsadar rayuwa.

Da ya ke jajiberan sallace kasuwar ta cika maƙil da mutane.

A kasuwar kaji kuwa hada-hada kawai ake yi tsakanin masu kawo kaji daga karkara zuwa masu saya su kai birane.

Ƙaramar kaza ita ce naira 1000
(ɗan tsako kenan) amma manyan kaji sun kai 7,000 zuwa 8,000 har zuwa 10,000.

Allah ya kawo mana sauƙi.

Amma kamar wasu kayan abincin suna ɗan rage kuɗi.

Tsaraba daga abokin aikina Idris Ibrahim Azare

Continue Reading

Kasuwanci

Matatar mai ta Ɗangote ta soma sayar da fetur a Najeriya

Published

on

Matatar mai ta Ɗangote da ke Najeriya ta fara sayar da fetur a ƙasar a ranar Talata, in ji ƙungiyar tallatawa da sayar da mai ta kamfanin.

Wannan babban matakin tsayawa da ƙafafu ga Najeriya wajen biyan buƙatar makamashi da take da ita.

Mutumin da ya fi kowa kuɗi a Afirka Aliko Ɗangote ne ya gina matatar man, mafi girma a nahiyar a gaɓar tekun Legas kan dala biliyan 20, kuma an kammala aikin bayan tsaiko na shekaru da dama da aka samu.

Matatar na iya tace gangar ɗanyen mai 650,000 kowace rana, kuma idan ta fara aiki ɗari bisa ɗari za ta zama mafi girma a Afirka da Turai.

KU KUMA KARANTA: Ɗalibi ya lashe N5 miliyan a tallan siminti na Dangote

Daraktan rukunan kamfanonin Dangote Devakumar Edwin ya tabbatar da cewa sun fara sayar da man dizel da man jiragen sama a ƙasar.

Edwin ya shaida wa Reuters cewa “Muna da isasshen mai. Ana jigilar man ta ruwa da ƙasa. Jiragen ruwa na bin layi ɗaya bayan ɗaya don ɗiban dizel da man jiragen sama.”

“Jiragen ruwa na ɗaukar lita miliyan 26, amma muna ƙoƙarin ganin an kawo jiragen da ke ɗaukar lita miliyan 37 don sauƙaƙa ayyukan.”

Ƙungiyar masu sayar da man ta amince kan sayar da kowacce litar dizel naira 1,225 bayan ƙulla yarjejeniya kan tsayar da farashi, in ji Abubakar Maigandi, Shugaban ƙungiyar Masu Sayar da Man Fetur Mai Zaman Kanta a Nijeriya.

Mambobin ƙungiyar na da gidajen mai kimanin 150,000 a faɗin Najeriya, in ji Maigandi.

Matatar mai ta Dangote na so ta kawo ƙarshen dogaro ga man da ake shigowa da shi daga ƙasashen waje da Najeriya ke yi.

Najeriya ce ƙasar da ta kowace yawan jama’a a Afirka, kuma tana kan gaba a tsakanin ƙasashen da ke fitar da albarkatun mai, amma tana sayo mai daga waje saboda ba ta da matatu.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like