Connect with us

Kasuwanci

Muna Kokarin Bunkasa Harkokin Kasuwancin Zamani Ne Tsakanin Najeriya Da Chadi – Ambasada Abubakar

Published

on

…Ya Yi Shuru Game Da Batun Ko Zai Tsaya Takarar Gwamna

Dag; Mustapha Imrana Abdullahi.

JAKADAN Najeriya a kasar Chadi kuma tsohon shugaban rundunar sojojin Saman Najeriya Mashal Sadiq Baba Abubakar mai ritaya ya ce ya halarci kasuwar duniyar kasa da kasa ne da ke ci a Kaduna domin kokarin ganin an bunkasa harkokin kasuwanci tsakanin Najeriya da kasar Chadi.

Sadiq Baba Abubakar, ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a harabar kasuwar, jim kadan bayan kammala taron bude kasuwar da wakilin shugaban kasa ya yi a ranar Asabar, amma dai yaki amsa tambayar manema labarai a game da rade- radin da ake yi cewa wai ya na son tsayawa takarar Gwamnan Jihar Bauchi.

Sai ya ce “mun zo nan ne domin maganar kasuwar duniya”.

Tsohon shugaban rundunar sojan Saman, wanda kuma a yanzu shi ne jakadan Najeriya a kasar Chadi, ya ce ya zo da wata tawaga ce ta yan kasuwa daga kasar Chadi domin tattaunawa a kan irin abubuwan kasuwancin da ya dace kasashen biyu su tattauna a kansu, inda ya tabbatar da cewa samun irin wannan damar zai sama wa kasashen biyu damar bunkasa harkokin kasuwanci a tsakaninsu.

Kamar yadda ya ce, “hakika a halin yanzu al’amari ne mai zaburarwa yadda duniya take gogoriyon ganin sun magance duk wani kalubale na gasa a batun ci gaba, don haka ne ma nake ganin taken kasuwar na Bana ya da ce.

“Duk lamari ne na ganin an kara zage damtse domin ganin tattalin arzikin Najeriya ya shiga jerin gogoriyon da kasashen duniya ke yi don ana bukatar hakan”.

“Don haka wannan rana mai matukar muhimmanci ce, saboda haka nake yaba wa wadanda suka shirya wannan kasuwa, wato cibiyar bunkasa harkokin kasuwanci ta Kaduna kuma ina saran za su leka sauran bangarori ma da nufin cin ribar da ke wurin, kuma zamu ga irin yadda za mu fadakar da jama’a su zama sun samo suna tare da tsarin

“Wannan shiri ne mai kyau, ..don haka kamar yadda na ce ne mun zo da tawaga daga kasar Chadi, wadanda suke da zimma domin sun ga akwai dama da yawa a nan. Muna fatan za su samu cikakkiyar damar cin moriyar abin da suke gani a nan”.

“Duk irin kokari da Zimmar da suke da ita, hakika zai taimaka wajen bunkasa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu wato Najeriya da Chadi”, inji Sadiq Baba Abubakar.

Da yake ci gaba da yi wa manema labarai jawabi kuma, Ambasadan ya ce a cikin harshen Hausa cewa “abu ne mai matukar farin ciki”.

“Wannan ne na farko da muka samu zuwa da wata tawaga daga kasar Chadi domin ganewa idanunsu abubuwan da za su amfani al’ummar kasarsu”.

“Kuma muna son mu gayyaci yan Najeriya zuwa Chadi domin suma su ga wadancan abubuwan da za su amfani jama’ar Najeriya, hakika wannan damace mai matukar muhimmanci.

Lokacin da aka yi masa tambaya a game da batun ko zai tsaya takara, sai ya ce ..”A’a …ai wannan batun kasuwar duniya ne muke yi kawai”.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasuwanci

Farashin kayan abinci daga kasuwar Anchau ta jihar Kaduna

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Farashin kayan abinci a jiya 23th April 2024

Masara
Me aure dubu 47 – 45 – 44
Marar aure dubu 42 – 41- 40

Farin wake
Dubu 90k 85k 80k

Waken suya
Dub 50k

Dawa
Dubu 43k 40k

Barkwano
Dubu 60k 57k

Tattasai
Busasshe dubu 70

Tumatir busasshe dubu
Dubu 70k

Tarugu
Dubu 45k 43k

KU KUMA KARANTA: Farashin kayan abinci a wasu kasuwanni a wannan makon

Shambo
Dubu 28k 27

Shinkafa me bawo
Dubu 40k 38k

Kwalin sugar mazarkwaila
Dubu 27k 26k
Karami dubu 17k 16k

Taki urea dubu 31k 30k
Indorama npk dubu 40k

Npk magic dubu 38k

Cement
Dubu 7100

Dauro
Dubu 55k 53k

Buhun fulawa
Dubu 53k

Buhun sugar
Dubu 77k

Kwalin taliya
Dubu 12,500

Indomie
Chaerie dubu 10,800
Supreme dubu 10,700

Macaroni dubu 12,500

Buhun dabino
Dubu 177k – 160k

Goriba
Dubu 13k – 12k

Kwanon rufi
Dubu 65 – 63

Abincin dabbobi

Dusa na inji menauyin 75kg Dubu 23 – 22k

Dusa tankaɗaɗɗiya menauyin 50kg dubu 14,000k

Garin Ɗorawa menauyin 65kg dubu 13k 14,500k

Kowa menauyin 35kg dubu 8k – 9k

Bincike da ƙwaƙƙwafi
Sarkin kasuwar Anchau

Continue Reading

Kasuwanci

Farashin kayan abinci a wasu kasuwanni a wannan makon

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

A kasuwar Bokkos da ke Jos, ranar Alhamis an sai da jar masara buhu ɗaya 50,000
Fara 48,000

Acca kwano ɗaya 3,200
Manya fara 3,100.

A kasuwar Mangu masara an sai da buhu ɗaya 51,000.

Haka aka sayar a kasuwar Barikin Ladi.

Kasuwar Azare jiya Lahadi.
An sayar da Dawa ja 56,000
Fara 54,000

Gero 56,000

Wake 95,000 zuwa
100,000.

Rogo busashshe 30,000 buhu ɗaya.

An sayar da buhun tsamiya 12,500.

An sayar da gyaɗa mai kwanso 30,000 buhu ɗaya.
Haka farashin ya kasance jiya a kasuwar Jama’are da kasuwar Sakuwa.
Shinkafa kuwa kwano ɗaya ‘yar ƙasa daga 3,000 ne zuwa 3,400.

KU KUMA KARANTA: Turkiyya na fatan bunƙasa kasuwanci da Saudiyya zuwa dala biliyan 30

Da muka leƙa kasuwar dabbobi kuwa an yi jugum-jugum tsakanin mai saya da mai sayarwa kowa yana kukan tsadar rayuwa.

Da ya ke jajiberan sallace kasuwar ta cika maƙil da mutane.

A kasuwar kaji kuwa hada-hada kawai ake yi tsakanin masu kawo kaji daga karkara zuwa masu saya su kai birane.

Ƙaramar kaza ita ce naira 1000
(ɗan tsako kenan) amma manyan kaji sun kai 7,000 zuwa 8,000 har zuwa 10,000.

Allah ya kawo mana sauƙi.

Amma kamar wasu kayan abincin suna ɗan rage kuɗi.

Tsaraba daga abokin aikina Idris Ibrahim Azare

Continue Reading

Kasuwanci

Matatar mai ta Ɗangote ta soma sayar da fetur a Najeriya

Published

on

Matatar mai ta Ɗangote da ke Najeriya ta fara sayar da fetur a ƙasar a ranar Talata, in ji ƙungiyar tallatawa da sayar da mai ta kamfanin.

Wannan babban matakin tsayawa da ƙafafu ga Najeriya wajen biyan buƙatar makamashi da take da ita.

Mutumin da ya fi kowa kuɗi a Afirka Aliko Ɗangote ne ya gina matatar man, mafi girma a nahiyar a gaɓar tekun Legas kan dala biliyan 20, kuma an kammala aikin bayan tsaiko na shekaru da dama da aka samu.

Matatar na iya tace gangar ɗanyen mai 650,000 kowace rana, kuma idan ta fara aiki ɗari bisa ɗari za ta zama mafi girma a Afirka da Turai.

KU KUMA KARANTA: Ɗalibi ya lashe N5 miliyan a tallan siminti na Dangote

Daraktan rukunan kamfanonin Dangote Devakumar Edwin ya tabbatar da cewa sun fara sayar da man dizel da man jiragen sama a ƙasar.

Edwin ya shaida wa Reuters cewa “Muna da isasshen mai. Ana jigilar man ta ruwa da ƙasa. Jiragen ruwa na bin layi ɗaya bayan ɗaya don ɗiban dizel da man jiragen sama.”

“Jiragen ruwa na ɗaukar lita miliyan 26, amma muna ƙoƙarin ganin an kawo jiragen da ke ɗaukar lita miliyan 37 don sauƙaƙa ayyukan.”

Ƙungiyar masu sayar da man ta amince kan sayar da kowacce litar dizel naira 1,225 bayan ƙulla yarjejeniya kan tsayar da farashi, in ji Abubakar Maigandi, Shugaban ƙungiyar Masu Sayar da Man Fetur Mai Zaman Kanta a Nijeriya.

Mambobin ƙungiyar na da gidajen mai kimanin 150,000 a faɗin Najeriya, in ji Maigandi.

Matatar mai ta Dangote na so ta kawo ƙarshen dogaro ga man da ake shigowa da shi daga ƙasashen waje da Najeriya ke yi.

Najeriya ce ƙasar da ta kowace yawan jama’a a Afirka, kuma tana kan gaba a tsakanin ƙasashen da ke fitar da albarkatun mai, amma tana sayo mai daga waje saboda ba ta da matatu.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like