Connect with us

Siyasa

Rashin Halaccin PDP A Jihar Taraba Yasa Ni Canza Sheka Zuwa APC – Sanata Bwacha

Published

on

Daga; Bashir Bello, Majalisa Abuja.

A BISA kokarin da suke na ganin cewa an tsabtace harkar siyasa a Jihar Taraba, wani jigon a Jam’iyyar PDP, Sanata Emmanuel Bwacha ya sauya sheka zuwa Jam’iyyar APC sakamakon irin rashin halaccin da ‘ya’yan Jam’iyyar ke nunawa yayin gudanar da al’amura a Jihar.

Da yake zantawa da manema labarai, Bwacha ya bayyana cewa shi halastaccen dan Jam’iyyar PDP ne amma ganin irin yadda al’amura suka sauya ba tare da nuna kishin al’umma ba kuma da nuna gaba yasa ya sama wa kansa sauki ta hanyar canza sheka izuwa Jam’iyyar APC.

Ya kara da cewa, dalilin da yasa ya bar Jam’iyyar PDP kamar yadda ya saba yin bayanai a yan kwanakin da suka gabata, dole ce ta sanya shi domin bai taba barin Jam’iyyar PDP ba, bai taba canza sheka ba daga PDP tun akalla shekaru 25 da na shige ta.

Ya ce “Dalilin da yasa na canza Jam’iyya na koma APC shi ne, a yanzu ba PDP da na sani bace wanda muka kafa, musamman a Jihar Taraba, yanzu PDP na da
shugabancin da ba don taimakon al’umma take yi ba, sai don son zuciya da shugabanci irin na fir’una wanda idan mutum ya tashi nuna maka wariya, sai ya ce yana maka na kyashi ne domin ya ga kana yi wa al’umma abubuwa masu kyau, domin kai kana kawo wa al’umma ayyuka dake faranta zukatansu.”

“Sai kaga shugaba na maka kyashi, yana maka kiyayya a sarari, idan ya zamana za ka Kaddamar da wasu ayyukan, duka wanda ke cikin Gwamnatin sai kaga sun ki zuwa wajen wanda abinda su basu iya yi ba a matsayin su wani na yi, amadadin kai kawai ka ce masa ka gode don yana sauke maka wani dawainiya, amma sai kaga mutum yana Kawo kishi da kiyayya.”

“Naga wannan yana Kawo banbance banbance tsakanina da magoya bayana dana Gwamna shi ne nace toh gara na tashi domin akwai rabe-raben kai, wanda har hakan ya kawo lokacin da aka shirya taron shugabancin Jam’iyyar ba a sanar da ni, bayan ba wani shugaban mazaba na Jam’iyyata ta PDP da bansan shi ba, domin wannan shi ne Jam’iyyar da nayi komai domin na tabbatar ya zauna a matakin Jaha.”

“Mu muka kawo Jam’iyyar mu ka yi wahalar da muka kafa tun lokacin Solomon har zuwa yau, toh sai wani kawai ya fito ba daga inda muka san shi ba yazo ya shiga don ya yi amfani da mu saboda ganin biyayya da muke da shi ga manyan mu suka ce mu Zabe shi, iyayen mu suka ce mu Zabe shi kuma muka Zabe shi, amma kawai sai muka zo muka gane cewa wannan mutumin karara ne muka zuba a kan mu wanda a yanzu halin da muke ciki, bama iya motsi, shi yasa yanzu gara na je na fake a wani waje na samu iska da yanci na kaina inyi siyasa na hankali Kwance.”

Acewarsa, tuntuni mutane al’ummarsa sun kwana biyu suna jiran ya fita daga PDP tun da jimawa tun kamin zaben da ya gabata na zaben 2019, kuma dalilin kuwa shi ne sun gane cewa Gwamnan Jihar na Kokarin ya fadi zaben shi yasa suka ce ya fita ya je ya canza wannan Jam’iyyar ta PDPamma yace zai tsaya.

Emmanuel Bwacha ya ci gaba da cewa, Gwamnan ya kawo Kwamishinan Kudi na Jihar ya tsaya takara da shi, amma da ya fadi sai ya koma ya sake mayar da shi bakin aikinsa, hakan yasa ya kawo wani daga Jam’iyyar APGA ya bashi damin Kudi da wani tsohon Sanata kuma tsohon minista, amma suka ka dashi don bai ma zo na biyu ba saboda Jam’iyyar APC ce ta biyu amma shi yazo na karshe yayinda shi yaci zaben.

Hakazalika, tun daga wannan lokacin ba zaman lafiya a tsakanin su amma yana hadiyewa ne da hakura, domin littafi mai tsarki ya nuna musu cewa suyi addu’a, toh amma yayi addu’ar yaga ba canji saboda idan kana hulda da mutumin da zuciyar shi kaman na Dutse take, kuma ya koma gefen iblis dole ka fita harkar shi.

“Lokacin da aka yi taron da ya fitar shugabannin wannan Jam’iyyar ta PDP, bai tuntube ni ba, yace duk wanda ya neme ni ya nemi shawara ta za a kore shi daga Jam’iyyar, kuma bansan waye shugaban Jam’iyyar na mazaba ta ba kuma ni mamba ne na manyan Jami’ai (NEC) na Jam’iyyar a matakin Kasa, sai naga shi ma baya bani hakkina kamar ko yana tsoron Gwamna ne ko ya bashi cin hanci ne, don haka naga gara na fita harkar su naje Inda mutuncina zai kasance a tsare, kuma zan zauna cikin lumana.”

“Halin da muke ciki a Jihar Taraba, kowa ya gaji, kowa yana kuka, shi yasa yanzu a ko wani irin Jam’iyya idan za a samu mutumin da zai yi adalci, za a kada wannan Gwamnatin Jihar balle ma a Jam’iyyar APC da take zuwa na biyu, kuma APC na da mutane a kasa, hakan yasa Kada Gwamnatin Jihar a lokacin Zabe ba zai zama matsala ba.”

“Ba ni da matsala da su. Kuma ku tuna, duk wani harka da za kuyi, kar kuyi zaton kowa zai so ku. Ba a rasa wadansu kalilan wadanda suke ganin a’a, saboda da an barni anan ne zai tsaya takara koda ba zai ci don ace za a iya bashi matsayin Minista, toh da akwai duk irin wadannan mun san da su amma mu muna so mu tsaya takara ne don mu ci, ba wai don sunan an tsaya Zabe ba, saboda haka irin wadannan suna nan sun tsaya a gefe da bakin ciki, kuma ta yiyu sune suke tura wadansu kalilan mutane suna Zage-zage, toh duk munsan da su amma duk ba zai dame mu ba domin burinmu shi ne mu ci Zabe kawai kuma idan Allah Ya yarda zamu ci.” Inji Shi

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like