NNPCL ya ɗora alhakin ƙarancin man fetur akan matsalolin tsare-tsare

0
115

Sanarwar da mai magana da yawun kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar tace, an warware matsalar.
Babban kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, ya bayyana cewar matsalolin tsare-tsare ne suka sabbaba dawowar dogayen layukan mai a wasu sassan ƙasar.

Sai dai sanarwar da mai magana da yawun kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar tace, an warware matsalar.

KU KUMA KARANTA:NNPC ta ƙara farashin man fetur a Najeriya

Sanarwar tace, “babban kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, na so ya bayyana cewar matsalolin tsare-tsare ne suka sabbaba matsalar ƙarancin man fetur da ake fama a wasu sassan ƙasar nan a halin yanzu, kuma an riga an magance ta.

“Kuma kamfanin yana son jaddada cewar farashin albarkatun man fetur na nan a yadda suke ba su sauya ba.”

Don haka NNPCL na ƙira ga ‘yan Najeriya da su kaucewa ɗabi’ar ɓoye man, kasancewar akwai wadatarsa a ƙasar”.

Leave a Reply