Connect with us

Noma

Muna Son Samun Sababbin Hanyoyin Noman Masara A Najeriya – Bello Annur

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

SHUGABAN masu kokarin habbaka Noman Masara a tarayyar Najeriya Alhaji Bello Abubakar Annur Funtuwa, ya bayyana kokarin da suke yi domin kara habbaka Noman Masara a fadin kasar baki daya da cewa domin dogaro da kai ne.

Alhaji Bello Abubakar Annur, ya shaidawa manema labarai hakan ne a lokacin da yake ganawa da su a wajen babban taron bitar da suka shiryawa mambobin kungiyar a Kaduna.

Alhaji Bello Annur ya ci gaba da cewa an shirya wannan taron fadakarwa da ake yi a yanzu haka a garin Kaduna ne domin fadakar da mambobinsu da kuma sauran manoma na kasa baki daya irin romon da ke tattare da yin amfani da fasahohin zamani wajen yin Noma.

“Kasancewar ba a dade da yin zaben sababbin shugabanni a kungiyar ba don haka aka ga ya dace a yi wa sababbin shugabannin taron bita domin kowa ya fadaka a game da Noman zamani da kuma hanyoyin da ya dace manoma su tunkara musamman masu Noman Masara”.

Ya kara da cewa taron kuma zai taimaka masu wajen sanin yadda za su tafiyar da shugabancin kungiyar kasancewa an yi sabon zaben shugabanni ne.

A game da batun matsalar tsaro kuwa, Bello Annur ya shaidawa manema labarai cewa, ” hakika kamar yadda kowa ya Sani akwai matsalar tsaro a kasa musamman a yankin arewacin Najeriya, amma duk da hakan an godewa Allah domin an yi Noma kuma an samu amfani kwarai duk da dai matsalar ta kasance wasu daga cikin manoman da suka fara aikin Gonar suna ji suna gani abin ya gagare su saboda irin yadda matsalar take tafiya, wasu sun bar Gonakan sun ta fi wasu kuma bayan sun yi Noman sun girbe amfanin Gonar amma su je su gyara shi sai lamarin ya zama wata matsala daban domin abin ya gagara, har wasu an Kona masu Gonakan kuma da yawa daga cikin manoman Masara abin ya shafe su saboda hakan zamu ce an samu matsaloli amma duk da hakan za mu ce sai godiyar Allah domin an yi Noman kuma an same shi”.

A game da batun Dalar Masarar da aka tara a Kaduna kuwa domin a kara wa manoma kwarin Gwiwar ci gaba da zage damtse domin Noma Masara kuwa, Bello Annur ya kara da bayanin cewa hakika an samu ci gaba kwarai a wajen batun Noman Masara domin na farko ma an samu yin Dalar Masarar fiye da irin wadda aka samu a bara, domin a ba na an samu yin Dala guda Ashirin da biyu da ake saran zuwan shugaban kasa domin ya kaddamar a Kaduna wanda hakan ba karamin ci gaba aka samu ba.

“Kuma duk Masarar da aka tara an karbo ta ne daga hannun Manoman da aka ba kayan Noma suka Noma kuma za a sayar wa masu kamfanonin sarrafa ta suma su ci gajiyar shirin da Gwamnati take aiwatarwa, duk kamfanin da aka Sayarwa zai Sanya wa Gwamnati kudin ta ne a cikin Banki kawai ya dauki Masara  ya ta fi da ita kamfaninsa domin ya sarrafa kasa da jama’arta baki daya su samu amfani kamar yadda duk dan kasa nagari ke bukata”. 

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Bagudu ya halacci taron bunƙasa harkar noma a Abuja

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Sanata Abubakar Atiku Bagudu ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren tattalin arziƙi na ƙasa a ranar Talata 16/04/2024, Ya halarci wani shiri na musamman a babban birnin tarayya Abuja domin bunƙasa sha’anin harkokin ayukkan gona a faɗin Najeriya.

Shirin wanda yake ƙarƙashin gwamnatin ƙasar Jamus (Germany ) da kuma ƙungiyar GIZ zai bayar da gagarumar gudumuwa wajen bunƙasa sha’anin ayukkan gona a Najeriya.

Bagudu ya bayyana alfanun da ke akwai ta haɗaka da ƙungiyoyi ire-irensu GIZ ta hanyar musayar ilmi da amfani da zamani wajen cimma manufa, Bagudu ya ƙarfafawa mutanen da suka halarci shirin da su rinƙa shirya taron ƙara wa juna sani domin cimma kyakkyawar manufar ciyar da ƙasa gaba.

KU KUMA KARANTA: Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Bagudu ya ƙara fayyace cewar haɗaka na da matuƙar muhimmanci domin ta hakan ne za’a samu ci gaba a fannin tattalin arziƙi da ci gaba a Najeriya.

Continue Reading

Labarai

Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Published

on

Wasu manoman tumatur a ƙaramar hukumar Bagwai ta jihar Kano, sun koka kan yadda tsutsa ke lalata musu amfanin gona.

Manoman sun ce sun yi asarar amfanin gona da ta kai kusan Naira miliyan 500. Sun kuma ce tsutsar ta shafi kusan hekta 1000 na gonakinsu.

Wani manomin tumatir, Bello Idris ya ce suna cikin wahalhalu kan yadda tsutsar ta addabe su.

”Za mu nome tumatir mu sayi taki 50,000, mu kuma sayi maganin feshi 10,000 da man fetur amma duk a banza,” in ji shi.

Ya yi ƙira ga gwamnati da ta kawo musu ɗauki da kuma gano inda matsalar take.

KU KUMA KARANTA: Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Haka-zalika, shi ma Sama’ila Bello mazaunin karamar hukumar Dawakin Tofa, ya ce tsutsar na lalata musu amfanin gona cikin lokaci kankani.

“Muna so gwamnati ta taimaka mana a duba a ɓangaren iri ne ko maganin feshi ne ba a sayar da mai kyau,” in ji Bello.

Continue Reading

Labarai

Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Published

on

Gwamnatin Kebbi ta ɓullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin sauƙaƙa musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farfaɗo da aikin noma domin jihar ta cigaba da riƙe kambunta a ɓangaren noman shinkafa a Najeriya.

Saboda haka ne ta gina ƙaramin wurin noma na zamani a ƙananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, ƙari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.

KU KUMA KARANTA: An ceto manoma 16 daga hannun masu garkuwa da mutane a Neja

Ya ƙara da cewa gwamnatin jiha ta biya kasonta na naira miliyan 350 a cikin shirin RAAMP, wanda zai samar da hanyoyin mota masu tsawon kilo mita 240 domin manoma su samu saukin sufuri, gwamnati ta sanya miliyan 350 a shirin.

Shehu Mu’azu ya sanar da hakan a taron manema labarai na sati-sati da ma’aikatar yada labarai ta shirya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like