Connect with us

Labari

Matsalar Tsaro: ‘Yan Bindiga Sun Jefa Al’ummar Yankunan Zamfara Da Katsina Cikin Mawuyacin Hali

Published

on

Daga Wakilinmu

h

Matsalar tsaro na ci gaba da tada hankula da daidaita al’umomi a yankunan arewacin Najeriya, baya ga mutanen da ke rasa rayuka ana kuma samun karin mutanen da ke gudun hijira.

Harin baya-bayanan da ya daidaita mutane da gidajensu shi ne wanda aka kai garuruwan Zamfara da Katsina a cikin wannan makon.

Ko a maraicen jiya Talata sai da ‘yan bindiga suka kai farmaki kauyen Hayin Dan Maciji na yankin karamar hukumar Gusau a Zamfara tare da hallaka mutane.

Sai dai yayin da ake cikin wannan yanayi su kuwa jama’ar garin garin Doma na jihar Katsina jajircewa suka yi, suka fatattaki wasu ‘yan bindiga da suka yi yunkurin kai masu hari.

Zuwa wayewar safiyar wannan Larabar mafi rinjayen jama’ar garin Hayin Dan Maciji na gundumar Ruwan Baure a yankin karamar hukumar Gusau, sun tsere zuwa wasu garuruwa makwabta.

Wani mutumin garin, wanda muka zanta da shi a kan hanyarsa ta gudun hijira, ya shaidawa BBC irin halin tashin hankalin da suka shiga:

”Muna cikin mawuyacin hali, da mu da iyalan mu da yara duk mun tarwatse, wasu ma ba su san inda ‘yan uwa da abokan arzikinsu suke ba.

Shiri na musamman da sashen Hausa na BBC zai dinga kawo muku kan cutar Coronavirus

Maharan sun kawo hari muna tsaka da sallar la’asar, su ka zo da manyan makamai, sun saba shigo mana amma wannan karon harbin mutane kawai suka dinga yi, kowa suka samu harba suke yi, wanda ya tsere to ya kuɓuta.

Kuma an ce su na can garin sun ja daga lamarin ya sha kanmu, ba mu san yadda za mu yi ba.”

Ita ma wata mata, mai ɗanyen goyo wadda ta gudu ta bar sauran ‘ya’yanta a garin na Hayin Dan Maciji, ta yi wa Wakilinmu karin bayani a kan hanyarta ta tserewa zuwa garin Kwatarkwashi.

Ta ce: ”To ni yanzu gani nan dai ban san abin da ake ciki ba, na baro gida babu shiri, kuma can na baro ‘ya’yana biyar ban san halin da suke ciki ba.

Da ta goye kawai na gudo, anan tare dani akwai mata sun kai goma da muka yo gudun hijira, mu na hanyar tafiya Kwatarkwashi, kuma da kafa muka yi tafiyar nan ta kusan mil ashirin, ba mu dauko komai ba.”

An kashe mutane da dama amma ban san adadinsu ba, sai dai an kai wasu da yawa asibiti, mu na cikin mawuyacin hali,” in ji matar da ba ta so a ambaci sunan ta ba.

To yayin da ake cikin wannan yanayi can a garin Doma na yankin karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, jama’a ne suka yi kukan kura, suka tunkari ‘yan bindigar da suka yi yunkurin kai masu hari a ranar Lahadin da ta gabata.

Wani mazaunin garin ya ce sun gaji da abin da ‘yan bindigar ke yi musu na kai hari ba gaira ba dalili, don haka suka dauki matakin rarakarsu.

”Sun yi kokarin su shiga gari Allah ya hana, matasa suka jajirce suka hana, ba mu da makamai sai adda da barandami, mu ka rarakesu, har bayan gari sun kashe mana mutum 10 da wasu 11 rauni, ba ma tsoron su sake dawowa mun dogara da Allah, jami’am tsaro mun kira su amma ba su zo ba sai kawai muka dauki matakin kare kan mu.”

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin SP Muhammad Shehu, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar Zamfara, da takwaran aikinsa SP Gambo Isa na jihar Katsina, kuma dukkansu sun ce za su bincika su kira mu.

Amma har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto ba mu ji daga gare su ba.

Jihohin Zamfara da Katsina na daga cikin wadanda ke fama da matsalar tsaro a arewacin Najeriya, inda ‘yan bindiga ke kai hare-hare da kashe mutane, da satar dabbobi da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

Al’ummar garuruwan jihohin na ci gaba da fuskantar matsaloli da yin gudun hijira suna barin dukiyoyinsu, ya yin da wasu rahotanni ke cewa ‘yan bindiga na dorawa mutanen haraji matukar su na son zaman lafiya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like