Connect with us

Labari

Kotu Ta Fara Sauraren Karar Mahadi Shehu Bisa Zargin Yada Takardun Bogi

Published

on

Daga; Mustapha Imrana Abdullahi.

BABBAR kotun tarayya da ke kano, ta fara sauraren shedu a tuhumar da ake yi ma Mahadi Shehu ta yada takardun bogi da yunkunrin tunzura jama’a a kan Gwamnatin Jihar Katsina ta hanyar amfani da kafar sadarwa ta yanar gizo.

A Ranar Litinin, 7 ga watan Fabreru na shekarar 2022, Babbar Kotun tarayya da ke Kano ta fara sauraren shedu a cikin karar da Babban Sufeton ‘Yan sandan Najeriya ya shigar yana tuhumar Mahadi Shehu da laifukan ya da takardun bogi da ke dauke da zarge-zargen almundahanar makudan kudade da ake zargin ka iya tunzura jama’a kan Gwamnatin Jihar Katsina a karkashin Gwamna Aminu Bello Masari.

A yayin zaman kotun, jagoran lauyoyin mai kara, Barista Lough, SAN (Babban Lauyan Najeriya), ya gabatar da Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina a matsayin sheda na farko wajen tabbatar da tuhumar da ake yi wa Mahadi Shehu.

Da ya mike domin bada shedar, ya soma da daukar rantsuwar bada sheda cewa zai fadi gaskiya tsagwaronta game da abin da ya sani a cikin wannan shari’ar.

Daga nan sai ya shaidawa Kotun sunansa; Mustapha Muhammad Inuwa, kuma shi ne Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina.

Lauya maigabatar da kara ya tambayi Mustapha Inuwa cewa, ya aka yi ya san Mahadi Shehu ya aikata abin da ake tuhumarsa akai?

Sakataren Gwamnatin ya amsa da cewa; Daraktan Watsa Labaransa mai suna Abdullahi Yar’adua ne ya ankarar da shi a kan wata tattaunawar da ake tuhumar ya yi (a cikin shirin Barka Da warhaka na ranar 2/7/2020) a gidan Radiyon Freedom FM da ke Kaduna, wadda kuma daga bisani ta yi ta yaduwa a gari kamar wutar daji, inda da farko a ciki yake ikirarin cewa jami’an gwamnatin jihar Katsina a karkashin Gwamna Aminu Masari sun yi facaka da kudade sama da Nera Biliyan 24 daga asusun tsaro na jihar.

Ya yi bayanin cewa, hakan ta sanya ya nemi kwafen wannan tattaunawa, shi ma ya saurara da kansa.

Sakataren Gwamnatin ya ce, daga cikin matakan da ya dauka don yin gyara a kan zarge-zargen da Mahadin ke yi, har da kiran taron manema labarai (wanda aka yi a cibiyar ‘yanjaridu ta gidan gwamnati).

Bugu da kari kuma, ya ce ya je har gidan Radiyon na Freedom FM, Kaduna inda har layin waya aka bude, mutane suka rika bugowa, suna yin tambayoyi, kuma a ciki ya musanta zargin yin almundahanar makudan kudaden da Mahadi, ke yadawa.

A cikin shirin, ya ce, ya yi bayani filla-filla dangane da kudaden da wanda ake tuhumar yake zargin wai an wawure inda ya jaddada cewa gwamnatin ba ta ma da wadannan kudin a asusunta na tsaro a jihar.

Bugu da kari, a cikin shirin ya ce, Mahadi, ya ambato sunayen wasu bankuna ciki kuwa har da “Fidelity” wanda sam – sam, gwamnati ba ta da asusun ajiya a bankin, amma Mahadi Shehu, har lambar asusun ya karanto, yana mai ikirarin cewa har ma da takardun yana da su a hannunsa.

Haka kuma, Sakataren Gwamnatin ya ce, ya musanta ikirarin da Mahadi, ya yi na cewa wai gwamnati ta fitar da tsabar kudi har Nera Miliyan 49 don sayen wayar salula guda 12 ga wakilan Majalissar tsaro ta jiha da kuma Nera Miliyan 849, 656, 000 wajen biyan kudaden alawus ga wasu jami’an ‘yan sanda 10, da suke gadi a wata tashar wutar lantarki da ke Lambar Rimi, yana mai ikirarin cewa har a lokacin da yake jawabin suna nan, suna aiki a wurin.

Mai bada shedar na farko, ya fada ma kotun cewa “na 1. wayar salular da Mahadi ke magana akai guda 50 ce aka saya ma ‘yan majalissar zarataswa ta jiha wadda ta kunshi kwamishinoni da masu ba gwamna shawara da sauransu ba Majalissar tsaro ba”.

“Na 2, ya ce jimlar kudin wayoyin (Nokia 3310), da na layukansu, da na tsarin abokan hulda na “CUG” da Kamfanin MTN ya kirkira masu, da cajin jerin lambobin da aka tsara masu da kuma kudin kati na tswon shekara daya duka jimlar Nera Miliyan 2,420,000 sabanin Nera Miliyan 49 da yake ikirari.

A kan batun lambar Rimi kuma, Mustapha Inuwa ya ce, sun iske gwamnatin da suka gada ta tura “yan sanda suna gadi a wurin tun cikin watan 12 na shekarar 2011, lokacin da aka sace wani Bature ma’aikacin kamfanin.

Kuma tun daga lokacin har zuwa watan Ogusta na 2017 da gwamnatin mai ci yanzu ta janye jami’an tsaron, tare da tsaida biyan kudaden saboda masu kamfanin sun dawo, jimlar abin da gwamnatocin biyu suka kashe ita ce Nera Miliyan 12,066,000 ba Miliyan 849,656 000 da yake yadawa ba.

Ya sheda ma Kotun cewa, duk da wannan matakin yin gyaran da gwamnatin ta dauka na yin bayanai tare da fito da sahihan takardun ta, a maimakon Mahadi, ya daina, sai ma ya kara fadadawa, ta hanyar ci gaba da wallafa jerin fayafayan bidiyo, (yana ba su suna) tun daga fitowa ta 1, har zuwa ta dari da wani abu.

Ya tabbatar ma Kotun cewa, irin bayanan da Mahadi, ya rika yi ya taba mutuncin gwamnatin da jami’anta, domin mutane sun sha bugo masu waya daga nan cikin gida da kuma kasashen waje, suna bayyana rashin jindadinsu dangane da abin da Mahadi, ke yada ma duniya cewa shi ne abin da ke faruwa a jihar Katsina.

Hakan ma in ji shi, ya sanya a wani lokaci ‘yayansu kan kasa fita zuwa makaranta saboda guje ma tsangwamar da abokansu ke yi masu bisa yarda da cin zarafin da wanda ake tuhumar ke yadawa a kan iyayensu.

Daga nan ne, sai Alkali ya tambaya cewa ko akwai wani abu da lauya zai nuna a matsayin shedar cewa eh! Lalle Mahadi Shehu ya aikata abin da shedar nasa ya fada?

Lauyan ya amsa cewa ba shakka akwai fayafayan hirar da Mahadi, ya rika yadawa da kwafen jawabin manema labarai wanda Sakataren Gwamnatin ya gudanar da kuma wasu jaridu da suka wallfa labarin.

Sai dai kuma, da aka nemi ya kawo su, Barista Lough ya ce sun manta ba su zo da su ba (abin da ya fusata ran mafi yawancin ‘yankallo), amma ya roki Kotun da ta ba su wata rana da za su kawo abin nunin shedar.

A yayin da Alkalin Kotun Mai shari’a A.A Liman, ya waiwayi jagoran Lauyoyin wanda ake tuhumar, Barista A.I Abubakar, ya amince da wannan bukatar, sai ya daga zuwa ranakun 28/2, da kuma 3/1/2022, domin ci gaba da sauraren shedun maigabatar da kara tare da cewa wanda ake tuhumar ya ci gaba da zama a kan beli har zuwa ranar da za a dawo kotu.

Sai dai wani abin da aka lura da shi a wannan karon shi ne, wanda ake tumar, Mahadi Shehu, dan Najeriya, dan asalin jihar Katsina, haifaffen kofar sauri, ya zo kotun tangaram, yana sanye da wando da taguwarsa mai gajeren hannu, farare wadanda da aka fi sanin shi da su, da ‘yar farar hularsa da kuma tabarau.

Kusan in baya ga takunkumin korona wanda kowa a cikin kotun yana na sanye da shi, bai zo da sandunan guragu, ko ya dauro janjami, ko wani abu da ya saba ma al’ada ba.

Hasali ma a wannan karon, akawun kotun na kiran sunasa a matsayin wanda ake tuhuma, sai ya yi zambur, ya mike, ya nufi akwatin da a kan saka wanda ake tuma, ya tsaya kyam, ya kuma yi kasake yana jin dukkan shedar da Dokta Mustapha Inuwa yake badawa, gaba da gaba dangane da abin da ake zarginsa da wallafawa.

“kowa ya debo da zafi bakinsa”.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like