Connect with us

Kudanci

Makarfi Mutum Ne Mai Magana Daya – Wike

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

GWAMNAN Jihar Ribas Nyeson Wike, ya bayyana Sanata Ahmad Muhammad Makarfi a matsayin mutum mai magana daya a koda yaushe.

Nyeson Wike ya bayyana hakan ne lokacin da ya kawo ziyarar girmamawa da kuma fatan alkairi ga Sanata Makarfi tun bayan da ya dawo daga kasar Ingila neman magani.

“Mun yi magana da shi ya ce Mani ya na Ingila neman magani, amma ya ce ga shi a Abuja duk da haka na gaya masa zan zo gida Kaduna in gan shi tun da ya dawo lafiya, muna godiya ga Allah da hakan”.

“Babban abin dubawa a halin yanzu shi ne yayan jam’iyya su samu hada kansu wuri daya ba maganar tsayawa takara ba ne lokaci zai zo nan gaba kadan, saboda koda an taayar da wani dan takara daga yankin Kudu ko Kudu maso Yamma idan ba a hada kan yan jam’iyya ba ta yaya za a samu nasara”, inji Wike.

Ya ci gaba da cewa jam’iyyar PDP ce yan Najeriya ke bukata domin ita ce ta dace da su, don haka a hadu wuri daya kawai ayi aiki tare domin na san Sanata Makarfi mutum ne mai kokari kwarai”.

“Kamqr dai yadda kowa ya Sani ba zamu bari kowa ya kashe kasar nan ba don haka aikin hadin kai ne kawai ya dace da mu baki daya”, inji Wike.

Da yake nasa jawabin Sanata Ahmad Muhammad Makarfi, cewa ya yi kamar yadda ya san Gwamna Nyeaon Wile da kokari hakika babu wanda zai dauke kokarin daga gare shi.

Makarfi ya ci gaba da cewa ya san lokacin da yake shugaban kwamitin rikon PDP Gwamna Wike ya yi duk abin da zai iya domin ya taimaka mana ni da kwamiti na, son haka zamu iya ci gaba da aiwatar da abin da muka yi kamar can baya da nufin samu mu lashe zabe.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Published

on

Wani jirgin sama mai sauƙar ungulu ya yi hatsari a yankin Ikeja da ke Jihar Legas a kudancin Najeriya.

Wani jami’in hukumar ba da agajin gaggawa ta Legas ya ce jirgin ya kama da wuta jim kaɗan bayan rikitowarsa da tsakar ranar Talata a kusa da filin jirgin sama na Murtala Muhammad.

KALLI CIKAKKEN BIDIYON ANAN:

Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, ‘National Emergency Management Agency’ (NEMA), ta ce mutum huɗu ne ke cikin jirgin kuma an ceto su da ransu.
Jami’in NEMA mai kula da sashen kudu maso yamma, Ibrahim Farinloye, ya ce ba su kai ga gano mamallakin jirgin ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Lamarin ya faru ne shekara uku bayan wani jirgin Helikwafta mallakar kamfanin Quorom Aviation ya faɗo a yankin Opebi na Legas ɗin a watan Agustan 2020.

Continue Reading

'Yansanda

Da wane dalili ‘yan sanda suka lakaɗa wa ɗan Okada duka a Legas?

Published

on

Wani ɗan Okada, mai suna Alasan Usman matashi mai ƙoƙarin neman na kansa domin rufawa kansa da ‘yan uwansa asiri.

A ranar jumu’a ‘yan sanda a jihar Legas suka tare shi suka ce ya kawo babur ɗinsa duk da dai bai san laifin da ya aikata ba, sai ya ƙi ya basu. Saboda ya ƙi basu suka masa duka sai kace ɓarawo sai da suka yi masa jina-jina yadda ba zai iya taɓuka komai ba, sannan suka tafi da mashin ɗinsa.

KU KUMA KARANTA: Ranar zuma ta duniya: Amfani da sirrikan dake tattare da zuma

Sai dai rahotanni sun tabbatar da cewa ‘yan Arewa mazauna Legas sun yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin an baiwa wannan ɗan Okada haƙƙinsa.

Yanzu haka shugaban hukumar ‘yan sanda na jihar Legas ya ziyarce shi a inda yake jinya, sannan an mayar masa da kuɗin belin da aka karɓa na mashin ɗinsa an kuma ba shi guduwmawa mai yawan gaske, kuma yana nan yanzu haka yana samun sauƙi sosai a unguwar Abbatuwa dake Legas.

Continue Reading

Hatsari

Fashewar bututun ɗanyen mai yayi sanadiyar mutuwar mutane 12

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da cewa mutane 12 ne suka mutu sakamakon fashewar magudanar mai a safiyar Juma’a a yankin Rumuekpe da ke ƙaramar hukumar Emoha a jihar.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, inda ta ce shaidar farko ya nuna waɗanda abin ya shafa na ɗiban ɗanyen man ne a lokacin da wurin ya kama wuta.

KU KUMA KARANTA: Kwastam ta kama tramadol ɗin naira miliyan 306 a Kaduna

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattaro cewa, hakan ya afku ne a yayin da wata motar bas ɗauke da ɗanyen mai ta kama wuta, yayin da take barin wurin zuwa wata matatar mai ta haramtacciyar hanya a yankin.

“Ya zuwa yanzu mutane 12 ana kyautata zaton sun ƙone kurmus. Har yanzu ba a gama sanin sunayen waɗanda abin ya shafa ba,” inji ta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like