Connect with us

Kudanci

Fulani Makiyaya Na Kokawa Da Tarar Naira Dubu 100 Ga Kowane Sa Da Aka Kakaba Musu A Kudanci

Published

on

Daga Wakilinmu

Tarar naira 100,000 ta hau kan kowacce Saniya da aka kama ta na gararanba a titi

Fulani makiyaya da ke kudancin Najeriya na kokawa kan sabbin dokoki da gwamnatin Delta ta kakaba musu da zai hanasu yawon kiwon sake.

Wannan na zuwa ne yayin da wa’adin da gwamnatin Delta ta sanya musu ke ciki, wanda ke nufin dokar da aka sanya tun a watan Satumbar bara na gab da soma aiki.

Dokar da majalisar dokokin jihar ta zartar ta ce idan aka kama makiyayi da dabbobinsa, za a ci shi tarar naira 100,000 kan duk saniya guda, da ƙarin wata 100,000 a kan mai saniyar har ma da ɗaurin shekara biyar zuwa goma.

Matakin da makiyayan ke ganin kokari ne na hana dabbobinsu sakat a sassan jihar. A wannan wata ne dai wa’adin da gwamnatin Delta ta ɗibar musu ke cika.

Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen jihar Delta, Alhaji Musa Muhammad, ya shaidawa BBC cewa a kullum cikin fargaba suke game da fargabar da suke ciki.

Ya ce fatansu shi ne a nunawa gwamnan jihar dokokin da ya ke kafa musu sun yi tsauri da yawa, sannan za su kawo musu matsala tsakaninsu da masu gonaki.

”Abinda na ke nufi shi ne baki dayan jihar Delta babu wani daji, hatta gidajen da muke zaune filayen mutane ne, cikin gonaki ne da sai an zo ana cirar rogo da sauransu.

Idan aka ce za a yi lissafi, a haka Shanun da suke nan, sun fi 500,000, a zo a ce ba za mu yi kiwo ba.

Dan hakan ne muke rokon gwamna yadda mu ke zaune lafiya da masu gonaki a taimaka a bar mu haka kafin abubuwa su tabarbare,” in ji Alhaji Musa.

Ya kara da cewa daman gwamnati na kiransu da jami’an tsaro domin a yi zama, duk lokacin da aka samu wata matsala ko bullar wata fitina.

Alhaji Musa ya ce dokokin da aka kafa na cewa su tsare Shanunsu babu zuwa ko ina kiwo sun yi tsauri ga batun cin tarar Saniya da batun idan an kama su da yawa za’a biya naira 500,000.

Sannan dokar ta tanadi cewa duk wanda ya gaza biyan wanann tara zai yi zaman kason shekara 5 ko 10, ga ka ai wannan abin damuwa.”

Shugaban ya ce inda kasar arewa suke, inda akwai dazuka, da wurin shan ruwa da dukkan abin da suke bukata da sauki, amma inda suke babu dazuka ko kaura za su yi babbar matsala hakan ke zame musu.

Batun rikici tsakanin fulani makiyaya da manoma kudancin Najeriya ya dade ya na ci wa ‘yan kasar tuwo a kwarya.

Sannan an jima ana ta kiraye-kiraye kan gwamnonin kudancin kasar su sake nazari kan haramcin kiwon sake da suka sanyawa fulanin da ke zaune a yankunansu.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sama mai sauƙar ungulu ya faɗo a Legas

Published

on

Wani jirgin sama mai sauƙar ungulu ya yi hatsari a yankin Ikeja da ke Jihar Legas a kudancin Najeriya.

Wani jami’in hukumar ba da agajin gaggawa ta Legas ya ce jirgin ya kama da wuta jim kaɗan bayan rikitowarsa da tsakar ranar Talata a kusa da filin jirgin sama na Murtala Muhammad.

KALLI CIKAKKEN BIDIYON ANAN:

Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, ‘National Emergency Management Agency’ (NEMA), ta ce mutum huɗu ne ke cikin jirgin kuma an ceto su da ransu.
Jami’in NEMA mai kula da sashen kudu maso yamma, Ibrahim Farinloye, ya ce ba su kai ga gano mamallakin jirgin ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Lamarin ya faru ne shekara uku bayan wani jirgin Helikwafta mallakar kamfanin Quorom Aviation ya faɗo a yankin Opebi na Legas ɗin a watan Agustan 2020.

Continue Reading

'Yansanda

Da wane dalili ‘yan sanda suka lakaɗa wa ɗan Okada duka a Legas?

Published

on

Wani ɗan Okada, mai suna Alasan Usman matashi mai ƙoƙarin neman na kansa domin rufawa kansa da ‘yan uwansa asiri.

A ranar jumu’a ‘yan sanda a jihar Legas suka tare shi suka ce ya kawo babur ɗinsa duk da dai bai san laifin da ya aikata ba, sai ya ƙi ya basu. Saboda ya ƙi basu suka masa duka sai kace ɓarawo sai da suka yi masa jina-jina yadda ba zai iya taɓuka komai ba, sannan suka tafi da mashin ɗinsa.

KU KUMA KARANTA: Ranar zuma ta duniya: Amfani da sirrikan dake tattare da zuma

Sai dai rahotanni sun tabbatar da cewa ‘yan Arewa mazauna Legas sun yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin an baiwa wannan ɗan Okada haƙƙinsa.

Yanzu haka shugaban hukumar ‘yan sanda na jihar Legas ya ziyarce shi a inda yake jinya, sannan an mayar masa da kuɗin belin da aka karɓa na mashin ɗinsa an kuma ba shi guduwmawa mai yawan gaske, kuma yana nan yanzu haka yana samun sauƙi sosai a unguwar Abbatuwa dake Legas.

Continue Reading

Hatsari

Fashewar bututun ɗanyen mai yayi sanadiyar mutuwar mutane 12

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da cewa mutane 12 ne suka mutu sakamakon fashewar magudanar mai a safiyar Juma’a a yankin Rumuekpe da ke ƙaramar hukumar Emoha a jihar.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, inda ta ce shaidar farko ya nuna waɗanda abin ya shafa na ɗiban ɗanyen man ne a lokacin da wurin ya kama wuta.

KU KUMA KARANTA: Kwastam ta kama tramadol ɗin naira miliyan 306 a Kaduna

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattaro cewa, hakan ya afku ne a yayin da wata motar bas ɗauke da ɗanyen mai ta kama wuta, yayin da take barin wurin zuwa wata matatar mai ta haramtacciyar hanya a yankin.

“Ya zuwa yanzu mutane 12 ana kyautata zaton sun ƙone kurmus. Har yanzu ba a gama sanin sunayen waɗanda abin ya shafa ba,” inji ta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like