Connect with us

Labari

Kungiyar Matan Fulani Sun Buƙaci Jami’an Gwamnati Da Su Daina Cin Zarafin Su

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WATA kungiyar matan fulani ta, Rube Fulbe Global Rights and Development Initiative, ta bayyana damuwarta kan yadda jami’an tsaro ke tafiyar da al’amura musamman ganin yadda aka yiwa wasu makiyaya fulani a wani faifan bidiyo na baya-bayan nan.

Da take zantawa da manema labarai a garin Kaduna, Shugabar kungiyar, Hajiya Halima Usman, ta ce dole ne su bayyana damuwarsu bisa la’akari da irin yanayin muguntar da aka yi wa mazajensu.

Ta ce “Mun zo nan ne domin nuna damuwarmu kan lamarin da ya faru makonni biyu da suka gabata a yankin Kakura da ke karamar hukuma chikun ta Jihar Kaduna inda aka yi kuskuren cewa wasu Fulani ‘yan fashi ne alhali ba su ba ne.”

Halima ta ci gaba da cewa, ba su ji dadin yadda jami’an tsaro ke jefa wadannan mutane cikin motar ba, suna daukar su tamkar dabbobi.

“Muna nan muna yi wa gwamnati kuka a matakin Tarayya da Jihar da ta yi taka-tsan-tsan da wannan lamarin, duba da irin muguntar da aka yi masu a lokacin da ake kiransu da ‘yan fashi.

Wannan dai ba shi ne karon farko da irin wannan lamarin ke faruwa ba, an dade ana tafkawa wanda a mafi yawan lokuta zaka ga ’yan banga suna far wa mazajenmu suna sace musu shanu, idan kuma suka rama ko yi kokarin karbo shanunsu, sai a bayyana su a matsayin ‘yan fashi. Ta ce

Ta yabawa gwamnatin Jihar Kaduna bisa matakin gaggawar da ta dauka duk da cewa mutanen nasu sun samu raunuka yayin da aka sako gawarwakin mutanen uku da aka kashe yayin harin kuma an yi musu jana’iza.

“Duk da haka, muna son gwamnati ta taimaka wa wadannan mutane ta hanyar biyan su diyya da aka yi musu ko kadan hakan zai rage musu radadin wahala.”

“Ta bayyana cewa, kalubalen da Fulani Makiyaya ke fuskanta a kasar nan shi ne yadda wasu jami’an tsaro ke kai wa al’ummarsu farmaki suna kwashe dabbobinsu, idan aka yi kokarin dawo da su, sai a bayyana su a matsayin ‘yan fashi.

“Wannan ba daidai ba ne, rayuwa fulani ba ta cikin aminci domin duk lokacin da wani abu ya faru za a rika zargin Fulani da aikatawa, rayuwarmu tana cikin hatsari don a mayar da fulani a rayuwar fulani kodayaushe ba a bakin komai ba, shi ya sa muke mika kokenmu, domin a karshe matan ke shan wuya ta yadda za a bar su ba abin da za su ciyar da iyalinsu.”

Daga nan sai Hajiya Halima ta bukaci gwamnati da ta kawo musu dauki musamman a kan matsalar satar shanu da ta ce a gaggauta magance ta.

Idan dai za a iya tunawa, sojoji da ‘yan sanda sun yi karin haske kan cewa mutanen da aka kama a wani faifan bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta a kwanakin baya, makiyaya ne da aka yi kuskuren cewa wasu ‘yan bindiga ne da suka kai hari a kauyen Kakura da ke karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna.

Taron ya samu halartar kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan, shugaban karamar hukumar Chikun, Engr. Salasi Musa, mamba mai wakiltar mazabar Chikun a majalisar dokokin jihar, Hon. Ayuba Chawaza, Hakimin Kujama, Stephen Ibrahim, da kwamandan rundunar soji ta 312, Laftanar Kanal D.O Igwilo.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like