Connect with us

Tattaunawa

Idan Matasan Najeriya Suka Rungumi Fanni Kafofin Sadarwar Zamani Za Su Sami Ayyukan Yi – Habibu Mu’azu

Published

on

Daga; Isah Ahmed, Jos.

HABIBU Mu’azu shi ne Daraktan cibiyar yada labarai ta kafofin sadarwar zamani na Enactifix da ke garin Jos. A wannan tattaunawa da ya yi da wakilinmu, ya bayyana cewa idan matasan Najeriya suka rungumi fanni kafofin sadarwa na zamani, zasu sami ayyukan yi.

Ga yadda tattaunawar ta kasance

GTK: Mene ne makasudin kafa wannan cibiya?

Habibu Mu’azu: Makasudin kafa wannan Cibiya, shi ne ganin yadda aka tafi aka bar Arewa a baya a bangaren harkokin sadarwar zamani ya sanya muka yi tunanin kafa wannan cibiya, musamman a wannan gari na Jos domin mu rika yada labarai na gaskiya, ba tare da nuna bangaranci ko banbancin addini ba. Kuma mun dauki lokaci muna shirin kafa wannan cibiya, domin mun fara shirin kafa wannan cibiya, tun shekara ta 2009. a lokacin na fahimci cewa lallai akwai bukatar al’ummarmu ta sami irin wannan cibiya.

GTK: Wadanne abubuwa ne wannan cibiya ta kunsa?

Habibu Mu’azu: A wannan cibiya muna daukar labarai tare da yada su. Kuma muna shirin rediyo da Talabijin, kuma dukkan abubuwan da muke yi, muna sanya su ne a kafofin sadarwar zamani na sada zumunta na yanar gizo.

GTK: Daga lokacin da kuka kafa wannan cibiya zuwa yanzu, ya kuka ga yadda mutane suke bibiyarku?

Habibu Mu’azu: Gaskiya mafiya yawan masu bibiyarmu matasa ne domin kusan dukkan shirye-shiryen da muke yi, sun shafi matasa ne. Don haka matasa ne suka fi bibiyarmu, kuma wadannan matasa sun hada da nan Najeriya da kuma kasashen waje domin muna da matasa da suke bibiyarmu a kasashen Libya da Amerika da Jamus da Saudiya da Sudan da Lebanon da dai sauransu.
Kuma muna watsa shirye – shiryenmu da harsunan Turanci da Hausa.

GTK: Kuna da ma’aikata guda nawa a wannan cibiya?

Habibu Mu’azu: Ya zuwa yanzu muna da ma’aikata kusan mutum 13, wadanda kullum suke fita su samo mana labarai.

GTK: Mene babban burinku kan wannan cibiya?

Habibu Mu’azu: Babban burinmu shi ne muga cewa al’ummarmu ta gyaru, ta dauki hanya ta cigaba.

GTK: A matsayinka na masani kan kafofin sada zumunta na zamani, ya kake ganin yadda wannan bangare zai kasance nan gaba?

Habibu Mu’azu: Wato kafofin yada labarai da muka saba da su a baya, kamar Rediyo da Talbijin da Jaridu, yanzu zamani yazo da wani canji kan wadannan kafofin yada labarai. Yanzu komai na labarai ya koma kan wadannan kafofin yada labarai na zamani na yanar gizo.

Yanzu labarai na komai ya koma wayar hanu kuma kullum abin gaba yake yi, don haka ina ganin nan gaba, wadannan kafofin yada labarai da muka sani a baya wato Rediyo da Talbijin da Jaridu za a neme su a rasa.

GTK: A matsayinka na masani kan kafofin sadarwa na zamani, wace gudunmawa ce kake ganin wannan fanni zai bayar wajen samar da ayyukan yi ga matasan kasar nan?

Habibu Mu’azu: Wato wannan fanni na kafofin sadarwa na zamani, a yanzu yana kan gaba wajen samarwa matasa ayyukan yi. Akwai sana’o’i da dama da mutum zai yi da waya wadanda nan take zasu kawo masa kudade.

A duniyar yanzu, akwai mutane da dama da suke sana’o’i na gaskiya bana damfara ba, ta wannan fanni. Babu shakka idan matasan Najeriya suka rungumi wannan fanni, na hanyoyin sadarwar zamani, zasu sami ayyukan yi. Matasa kada su damu da cewa sai sun yi aikin Gwamnati, domin yanzu duk matashin da ya ce yana jiran aikin Gwamnati, yana yaudarar kansa ne.

Matasa su shiga kafofin sadarwar zamani zasu sami ayyukan yi domin yanzu idan ka dubi masu kudin duniya, zaka ga cewa masu harkokin kasuwanci ne a kafofin sadarwar zamani. Misali kamar Elon Reeve Musk da Jeff Bezos mai kamfanin Amazon da Mark Eliot Zuckerberg mai shafi Facebook, duk sun sami kudadensu ne ta hanyar kafofin sadarwar zamani.

GTK: Wanne kira ne kake da shi zuwa ga Gwamnati da al’ummar Najeriya, kan wannan fanni na kafofin sadarwar zamani?

Habibu Mu’azu: Ina kira ga Gwamnatoci kan su samar da cibiyoyin horar da ilmin kafofin sadarwar zamani, saboda mahimmancin da wannan fanni yake da shi. Kuma ina kira ga Gwamnatoci su sanya a rika koyar da wannan fanni a makarantunmu, domin matasa su koyi wannan fanni kamar yadda ya kamata

Kuma ina kira ga al’ummar Najeriya musamman na Arewa, mu farka daga barcin da muke yi kan wannan fanni na kafofin sadarwar zamani.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

NTA Hausa za ta tattauna da shugaban jaridar Neptune, Dr. Hassan Gimba

Published

on

NTA Hausa Channel 165 a dandamalin Startimes DTT da dikoda Arabsat/Nilesat za ta kawo maku shirin “Bakin Zare” kai tsaye tare da Dr. Hassan Gimba Shugaban Kamfanin Jaridar Neptune Prime.

Dr. Hassan shahararren marubuci, ɗan jarida kuma ƙwarrare mai sharhi kan al’amurran yau da kullum.

Rana: Alhamis, 28th December 2023

Lokaci: 8.00pm

Zamu yi bitar shekara ta 2023 da sharhi kan mahimman abubuwan da suka faru a shekarar.

Ku kasance tare da mu, don jin yadda tattaunawan zata kasance.

Continue Reading

Kasuwanci

Menene manhajar ‘Kapo drive’?

Published

on

Wanda ya ƙirƙira manhajar ‘Kapo drive’ ya ziyarci ofishin jaridar Neptune Prime dake Abuja, inda ya gana da shugaban Neptune Prime, Dr. Hassan Gimba.

Neptune Hausa ta tattauna da ya ƙirƙiro manhajar ‘Kapo drive’, ga yadda tattaunawan ta kasance:

Neptune Hausa – Tarihin rayuwar ka

Muktar – Sunana Muktar Auwal, an haife ni a jihar Yobe, shekaruna 26. Nayi firamare da sakandare a garin Abuja da jihar Kano, nayi jami’ar El-Razi dake ƙasar Sudan, na karanci Ilimin Kasuwanci da Ilimin Lissafin Kuɗi.

Neptune Hausa – Menene manhajar Kapo drive?

Muktar – Manhaja ce da za ta sauƙaƙa tafiye-tafiye, da kuma farashi mai rahusa. Kuma muna so mu ga mun zarce sauran manhajar tafiye-tafiye, wanda ba na ƙasan nan bane, suna kuma chaji kashi 25 cikin 100, wannan ‘Kapo drive’ in na ɗan ƙasa ne kuma muna chaji kashi 10 cikin 100. Za mu rage matasa masu zaman banza, da samar musu da abin yi.

Neptune Hausa – Manhajar a duk Najeriya ce ta ke aiki?

Muktar – A yanzu a jihohi biyu ne, garin Abuja da jihar Kano. Amma muna sa ran a wasu jihohin nan ba da jimawa ba.

Neptune Hausa – Yanzu kamar motoci nawa kuke da su?

Muktar – Muna da motoci ɗari a yanzu, hamsin a garin Abuja, hamsin a jihar Kano. Amma muna sa ran ƙara motoci cikin wata uku da fara aiki. Kuma App ɗinmu ‘bridge’ ne wanda zai yi haɗa fasinjoji da direbobi. Wajen rajista akwai na fasinjoji da kuma na direbobi.

Neptune Hausa – Me ya jawo ra’ayin ka akan manhajar?

Muktar – Rashin abin yi ga matasa ne ya janyo ra’ayi na, da kuma rashin ilimin kimiyya da fasaha a jihohin arewa. Ina sa ran cire dubban mutane daga cikin wannan matsalar. Wannan manhajar zai samar da aikin yi ga mutum sama da dubu goma cikin wata uku.

KU KUMA KARANTA: Manhajar ‘Threads’ da yadda ake amfani da ita

Neptune Hausa – Yaushe za a fara anfani da manhajar?

Muktar – Za mu fara amfani da shi a garin Abuja a ranar 15 Disamba, 2023.
A jihar Kano kuma ranar 17 Disamba, 2023 da yardar Allah. Daga wannan ranar zaka sami manhajar a Play store, Apple store, IOS.

Muktar Auwal

Neptune Hausa – Kana da masu ɗaukan nauyin wannan manhajar ne?

Muktar – Ni kaɗai ne, bani da wanda ke ɗaukan nauyin. Amma ina so in akwai masu ɗaukan nauyin, ina maraba da su.

Neptune Hausa – Me burin ka?

Muktar – Ina son na faɗaɗa wannan manhajar ta isa duk jihohin arewacin Najeriya. Da kuma buɗe iyakoki a duk jihohin.

Neptune Hausa – Akwai abubuwan da za mu tsammani nan gaba?

Muktar – Ƙwarai kuwa, ina sa ran ƙara motoci wanda zai dinga tafiye-tafiye daga gari zuwa gari. Da kawo bas na ɗaukan mutane dayawa.

Neptune Hausa – Daga ƙarshe me za ka ce?

Muktar – Ina godiya ga Allah da ya bani damar buɗe wannan manhajar, ina kuma kira ga matasa musamman ƴan arewa da kada su karaya a burikan su.

Neptune Hausa – Mungode da bamu lokacin ka.

Muktar – Ni ma nagode.

Continue Reading

Labarai

Shugaban Daylight Reporters ya ziyarci ofishin Neptune Prime a Abuja

Published

on

Babban jami’in gudanarwa na kamfanin dillancin labarai na jaridar yanar gizo ‘Daylight Reporters’ Ɗahiru Hassan Kera, ya kai ziyarar girmamawa ga ofishin kamfanin Neptune Network Nigeria Limited, mawallafin jaridar Neptune Prime sashen Turanci da Hausa Dakta Hassan Giɓma ne ya tarbe shi a babban ofishinta dake Abuja.

A lokacin ziyarar, Kera da Dakta Hassan Gimba, Mawallafi kuma Shugaban Kamfanin Neptune Network Nigeria Limited wanda kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Mabambantan Arewa-maso-Gabas, sun tattauna yadda za a ba da gudummawar ci gaba da kuma ci gaban yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

KU KUMA KARANTA: Shugaba kamfanin Neptune prime, Hassan Gimba, ya taya Gwamna Buni murnar sake lashe zaɓe

Kera wanda ya fito daga jihar Gombe kuma shugaban ƙungiyar malaman sadarwa da ƙwararru ta Nijeriya (ACSPN) daga yankin Arewa maso Gabas, ya jaddada muhimmancin magance matsalolin da yankin arewa maso gabas ke fuskanta domin ta haka ne kaɗai zai iya bunƙasa ƙasar nan.

Ya bayyana buƙatar saka hannun jari a ɓangaren ababen more rayuwa, kamar kyawawan hanyoyi, wuraren kiwon lafiya, da cibiyoyin ilimi. Shugabannin biyu da suka fahimci ƙalubalen da yankin ke fuskanta na ganin cewa, haɗin gwiwa kan wani shiri na bunƙasa yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya wani mataki ne mai kyau na magance ƙalubalen da yankin ke fuskanta, da kuma bayar da gudumawa ga ci gaban Nijeriya baki ɗaya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like