Connect with us

Tattaunawa

Bola Ahmad Tinubu Shi Ya Fi Cancanta Da Gadar Shugaba Buhari – Inji Abdullahi Kabir

Published

on

Daga; Sani Gazas Chinade, Damaturu.

A TATTAUNAWAR da gidan Jaridar Gaskiya Tafi Kwabo (GTK) ta yi da wani matashi kuma kusa a jam’iyyar APC mai mulkin kasar nan a garin Azare cikin karamar hukumar Karagum a Jihar Bauchi, Malam Abdullahi Kabir, dangane da danbarwar da ake kokarin farawa na lalubo wanda zai maye gurbin Shugaba Buhari idan wa’adin sa na barin mulki ya cika a shekara mai kamawa ta 2023 in rai ya kai, matashin ya fito karara ya bayyana cewar a ganinsa babu wanda ya ke ga ya cancanta da gadar shugaba Buhari fiye da jagoran jam’iyyar APC na kasa tsohon gwamnan Lagos Bola Ahmad Tinubu. Asha karatu lafiya.

GTK: Muna so ka dan tsakurowa masu karatu tarihin ka a takaice?

Abdullahi:- To ni dai Suna na Abdullahi Kabir, ni dan Jam’iyyar APC ne daga Azare karamar hukumar katagum dake Jihar Bauchi. A baya na yi takarar kujerar dan majalisar dokoki mai wakiltar mazabar Azare/Madangala a 2015, kana na zama mamba na kungiyar Buhari Organization tun daga 2002 zuwa 2007 tare kuma da rike mukamin CPC Awareness Forum.

Baya ga haka kuma na rike mukamin sakataren Jihar Bauchi na kungiyar Nigeria Consolidation Ambassadors Network (NCAN) kungiyar da suka sayawa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Form na tsayawa takarar Shugaban Kasa a 2019. Hakazalika na zama mamba na presidential campaign council a bangaren field operation duka dai a shekarar ta 2019. A Takaice ke nan.

GTK: Toh kasantuwar gashi wa’adin mulkin Shugaban Buhari ya kusa kaiwa karshe, shin wa kake ganin ya dace da gadonsa a wannan matsayi?

Abdullahi:- Alal hakika in aka lura da yadda shi Tinubu ya bada gudummawa wajen kaiwa ga nasarar shugaba Buhari da Jam’iyyar hadaka ta APC a zabukan 2015 da 2019 na ke ganin a daidai wannan lokaci babu wanda ya cancanta ya zama dan takarar Shugaban Kasa a Jam’iyyar APC a zabe mai zuwa 2023 da zai maye gurbin shugaba Buhari kamar Asiwaju Bola Ahmad Tinubu Jagaban Burgu Jagoran Jam’iyyar APC na Kasa tsoron Gwamna Jihar Legas.

Dalilina na fadar hakan kuwa shi ne, shi Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya dade yana bada gudunmuwa mai tsoka a siyasar Najeriya tun ma kafin kafa Jam’iyyar mu ta APC domin ya kawo cigaba sosai a Jihar Legas a lokacin da ya ke Gwamnan Jihar Legas tare kuma da bunkasa tattalin arziki Jihar ta Legas ta hanyoyi da dama da suka hada da bunkasa hanyoyin kudin shiga ta yadda ba sai Jihar Legas ta dogara da kudeden da Gwamnatin tarayya ke bada wa ba. Sanin kowa ne Jihar Legas ita babban cibiyar kasuwanci ce a kasar Najeriya.

GTK:- A matsayin ka na dan Arewa, ko kana ga yankin ka ya amfana da gudummwar Tinubu?

Abdullahi:- Kwarai da gaske yankin mu na Arewa ya amfana da gudummawar Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ta fuskoki da dama kuwa da suka hada da: Goya baya ga dan Arewa don ganin mulkin kasa ya dawo Arewa da karfin sa, Jama’arsa da dukiyar sa a yayin da Arewan ke da bukatar hakan a 2015.

“Ba nan ya tsaya ba har ila yau ya kuma bada gudumawarsa ga ‘yan Arewacin Najeriya a sauran zabukan 2007 da 2011 hade da zabukan shekarar 2015 da 2019 wadda hakan ne ya sake tabbatar mana cewar, lalle Tinubu masoyin Arewa ne na hakika wabda ke da bukatar mu saka masa.”

Kuma ma ai a zaben shekarar 2007 ya bawa tsohon mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar goyon baya a takarar sa da ya tsaya a Jam’iyyar AC ta Asiwaju Bola Ahmad Tinubu, hakazalika a 2011 ya sake bada gagarumin gudummawa ga Malam Nuhu Ribadu a lokacin da ya tsaya takarar Shugaban Kasa a Jam’iyyar ACN a 2011. Asiwaju Bola Ahmad Tinubu bai gajiya ba sai dai ya bada gudunmuwa na kafa Jam’iyyar APC wanda a yau take jagorancin kasa.

Kuma Shi ne wanda ya soma tasowa tare da dukkan manyan jiga-jigan Jam’iyyar ACN zuwa garin kaduna don gabatar da tayin yin hadaka na jam’iyyun adawa don su hade guri daya don su tunkari Jam’iyyar PDP mai mulki a wancan lokacin aka kuma kai ga nasarar kamar yadda na fada a baya.

GTK:- Ko wace rawa gwanin naka ke takawa wajen tallafawa daidaikun al’umma?

Abdullahi:- A gaskiya a yanzu a sanina kaf ‘yan siyasar mu a Najeriya babu wanda ya kai shi gina mutane a siyasance, kuma babu wanda ya kai shi sanin yadda za a magance matsalolin mu na siyasa da ma wadda ba na siyasa ba kaman sa, tabbas idan ya zama dan takarar Shugaban Kasa ba zai yi wahalar tallatawa ba cikin sauki Jam’iyyar APC za ta samu gagarumin nasara na lashe zabe cikin kankanin lokaci kuwa wadda kan hakan ne ma a zancen da na ke yi a yanzu haka tuni na rubuta wani littafi a kan tarihinsa da gwagwarmayar sa da zan kaddamar da shi nan da ‘yan kwanakin nan a Arewa House a garin Kaduna Insha Allah.”

GTK:- Me ya jawo hankalin ka na rubuta wannan littafi a kan Asiwaju Bola Ahmad Tinubu?

Abdullahi:- A hakikanin gaskiya na rubuta wannan littafi nawa ne bisa lura da yadda ya bada gudumawarsa a fannoni da dama da suka hada da siyasa da ayyukan cigaban kasa da sauran su ya sa naga ya dace na rubuta littafi wanda ya kunshi nasarorin sa da gudumawar da ya bayar a siyasance saboda kada tarihi ya manta da shi.

“Kuma na yi nazari sosai a kai sannan na ga ya kamata na rubuta littafi a harshen Hausa don mutanen Arewacin Najeriya su fahimci waye Asiwaju Bola Ahmad Tinubu sosai kasancewar Arewacin Najeriya ita ce yankin da ya fi ko ina yawan al’umma mai dauke da Jihohi akalla 19 banda Abuja babban Birnin Tarayyar kasar nan.”

GTK: A matsayin ka na jigo a Jam’iyyar APC me za ka ce kan rikicin cikin gida wanda yanzu haka ya baibaiye Jam’iyyar ta ku ta APC?

Abdullahi: To a gaskiya ni a ganina wannan rikicin da yake faruwa a Jam’iyyar APC ba komai bane illa cikar Jam’iyya domin babu yadda Jam’iyya za ta cika sosai ba tare da samun matsaloli ba nan da can kasancewar in dambu ya yi yawa baya jin mai, to amma duk da haka za a shawo kan matsalolin in Allah yaso wadda a karshe zai zama mana alheri.”

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

NTA Hausa za ta tattauna da shugaban jaridar Neptune, Dr. Hassan Gimba

Published

on

NTA Hausa Channel 165 a dandamalin Startimes DTT da dikoda Arabsat/Nilesat za ta kawo maku shirin “Bakin Zare” kai tsaye tare da Dr. Hassan Gimba Shugaban Kamfanin Jaridar Neptune Prime.

Dr. Hassan shahararren marubuci, ɗan jarida kuma ƙwarrare mai sharhi kan al’amurran yau da kullum.

Rana: Alhamis, 28th December 2023

Lokaci: 8.00pm

Zamu yi bitar shekara ta 2023 da sharhi kan mahimman abubuwan da suka faru a shekarar.

Ku kasance tare da mu, don jin yadda tattaunawan zata kasance.

Continue Reading

Kasuwanci

Menene manhajar ‘Kapo drive’?

Published

on

Wanda ya ƙirƙira manhajar ‘Kapo drive’ ya ziyarci ofishin jaridar Neptune Prime dake Abuja, inda ya gana da shugaban Neptune Prime, Dr. Hassan Gimba.

Neptune Hausa ta tattauna da ya ƙirƙiro manhajar ‘Kapo drive’, ga yadda tattaunawan ta kasance:

Neptune Hausa – Tarihin rayuwar ka

Muktar – Sunana Muktar Auwal, an haife ni a jihar Yobe, shekaruna 26. Nayi firamare da sakandare a garin Abuja da jihar Kano, nayi jami’ar El-Razi dake ƙasar Sudan, na karanci Ilimin Kasuwanci da Ilimin Lissafin Kuɗi.

Neptune Hausa – Menene manhajar Kapo drive?

Muktar – Manhaja ce da za ta sauƙaƙa tafiye-tafiye, da kuma farashi mai rahusa. Kuma muna so mu ga mun zarce sauran manhajar tafiye-tafiye, wanda ba na ƙasan nan bane, suna kuma chaji kashi 25 cikin 100, wannan ‘Kapo drive’ in na ɗan ƙasa ne kuma muna chaji kashi 10 cikin 100. Za mu rage matasa masu zaman banza, da samar musu da abin yi.

Neptune Hausa – Manhajar a duk Najeriya ce ta ke aiki?

Muktar – A yanzu a jihohi biyu ne, garin Abuja da jihar Kano. Amma muna sa ran a wasu jihohin nan ba da jimawa ba.

Neptune Hausa – Yanzu kamar motoci nawa kuke da su?

Muktar – Muna da motoci ɗari a yanzu, hamsin a garin Abuja, hamsin a jihar Kano. Amma muna sa ran ƙara motoci cikin wata uku da fara aiki. Kuma App ɗinmu ‘bridge’ ne wanda zai yi haɗa fasinjoji da direbobi. Wajen rajista akwai na fasinjoji da kuma na direbobi.

Neptune Hausa – Me ya jawo ra’ayin ka akan manhajar?

Muktar – Rashin abin yi ga matasa ne ya janyo ra’ayi na, da kuma rashin ilimin kimiyya da fasaha a jihohin arewa. Ina sa ran cire dubban mutane daga cikin wannan matsalar. Wannan manhajar zai samar da aikin yi ga mutum sama da dubu goma cikin wata uku.

KU KUMA KARANTA: Manhajar ‘Threads’ da yadda ake amfani da ita

Neptune Hausa – Yaushe za a fara anfani da manhajar?

Muktar – Za mu fara amfani da shi a garin Abuja a ranar 15 Disamba, 2023.
A jihar Kano kuma ranar 17 Disamba, 2023 da yardar Allah. Daga wannan ranar zaka sami manhajar a Play store, Apple store, IOS.

Muktar Auwal

Neptune Hausa – Kana da masu ɗaukan nauyin wannan manhajar ne?

Muktar – Ni kaɗai ne, bani da wanda ke ɗaukan nauyin. Amma ina so in akwai masu ɗaukan nauyin, ina maraba da su.

Neptune Hausa – Me burin ka?

Muktar – Ina son na faɗaɗa wannan manhajar ta isa duk jihohin arewacin Najeriya. Da kuma buɗe iyakoki a duk jihohin.

Neptune Hausa – Akwai abubuwan da za mu tsammani nan gaba?

Muktar – Ƙwarai kuwa, ina sa ran ƙara motoci wanda zai dinga tafiye-tafiye daga gari zuwa gari. Da kawo bas na ɗaukan mutane dayawa.

Neptune Hausa – Daga ƙarshe me za ka ce?

Muktar – Ina godiya ga Allah da ya bani damar buɗe wannan manhajar, ina kuma kira ga matasa musamman ƴan arewa da kada su karaya a burikan su.

Neptune Hausa – Mungode da bamu lokacin ka.

Muktar – Ni ma nagode.

Continue Reading

Labarai

Shugaban Daylight Reporters ya ziyarci ofishin Neptune Prime a Abuja

Published

on

Babban jami’in gudanarwa na kamfanin dillancin labarai na jaridar yanar gizo ‘Daylight Reporters’ Ɗahiru Hassan Kera, ya kai ziyarar girmamawa ga ofishin kamfanin Neptune Network Nigeria Limited, mawallafin jaridar Neptune Prime sashen Turanci da Hausa Dakta Hassan Giɓma ne ya tarbe shi a babban ofishinta dake Abuja.

A lokacin ziyarar, Kera da Dakta Hassan Gimba, Mawallafi kuma Shugaban Kamfanin Neptune Network Nigeria Limited wanda kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Mabambantan Arewa-maso-Gabas, sun tattauna yadda za a ba da gudummawar ci gaba da kuma ci gaban yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

KU KUMA KARANTA: Shugaba kamfanin Neptune prime, Hassan Gimba, ya taya Gwamna Buni murnar sake lashe zaɓe

Kera wanda ya fito daga jihar Gombe kuma shugaban ƙungiyar malaman sadarwa da ƙwararru ta Nijeriya (ACSPN) daga yankin Arewa maso Gabas, ya jaddada muhimmancin magance matsalolin da yankin arewa maso gabas ke fuskanta domin ta haka ne kaɗai zai iya bunƙasa ƙasar nan.

Ya bayyana buƙatar saka hannun jari a ɓangaren ababen more rayuwa, kamar kyawawan hanyoyi, wuraren kiwon lafiya, da cibiyoyin ilimi. Shugabannin biyu da suka fahimci ƙalubalen da yankin ke fuskanta na ganin cewa, haɗin gwiwa kan wani shiri na bunƙasa yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya wani mataki ne mai kyau na magance ƙalubalen da yankin ke fuskanta, da kuma bayar da gudumawa ga ci gaban Nijeriya baki ɗaya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like