Connect with us

Sana'o'i

Fawa Ba Karamar Sana’a Ba Ce -Sarki Lawal

Published

on

Musa Muhammad Kutama Daga , Kalaba

Sana’ar Fawa Sana’a ce mai  tarihi da kowace al’umma suke da masu yin ta mahauta kamar yadda aka sansu a jimlatance sun kunshi masu  fawar awaki da kuma shanu da sauran nau’ikan dabbobi .

Sarautar Fawa itama sarauta ce da take da nata sarki wato sarkin Fawa .

Aikin sarkin Fawa shi ne warware rikici Fawa,tsakanin mahauta  su ya su da kuma tsakanin mahauci da bafulatani ko ai dabba.

Domin jin yadda sarautar Fawa take a kudu, Alhaji Lawan Ibrahim  Isa sarkin Fawan Obubra kuma sarkin yakin Hausawan Kuros Riba ya yi wa wakilinmu karin bayani  domin jin yadda Fawa ta shigo Kuros Riba ,kalubalen ta da kuma yadda ma ake yin Fawar a kuros riba.Ya yi karin haske a kan haka

* Alhamdulillah wato kusan sana’ar Fawa ko shugaban cin fawa a kudancin Najeriya, ko a nan kuros riba  jihadi ne .* Kazalika ya ci gaba da cewa * Hakan yake nufi a matsaynka na shugaba ya zama wajibi ka tsaya ,ka tsare ka tabbatar cewa musamman Naman saniya Duk Inda bahaushe ya shiga  zai ci Naman saniya idan ya tambaya wane nama ne aka ce Masa Naman saniya zai Fara samun natsuwa cewa wannan Naman saniya  daga hannun musulmi ya fito suke sarrafa shi don haka zai samu natsuwa da shi fiye da kowane nama

Don haka a matsayin ka na .shugaba dole ka yi jihadin ka tabbatar da cewa duk wani nama na saniya da aka san tsarkakakke ne an yanka shi ya samu shaida cikakkiya .

Sarkin Fawan ya kkara da cewa ” Ita sana’ar Fawa kasan ita sana’a ce tun zamanin Annabawa akwai ta sannan duk inda za ka ga Fulani suna tafiya idan suka zo gari suka leka suka ga babu mahauci ba su zama garin saboda idan dabbarsu ta kasa wa zai gyara masu son haka sana’ar Fawa tana daya daga cikin dadaddiyar sana’a da ta fara shigowa kurmi “inji shi 

A cewar Alhaji  Lawan Isa ya ci gaba da cewa mahauta ‘yan asalin Arewa da suka shigo kuros riba sun isle ‘yan asalin jihar su ma na da nasu mahautan sai dai yanayin fawar ce ta banbanta da tasu “Eh ! Sun tarar da su su ma suna da nasu mahautan irin nasu maharba ,idan sun harbo naman daji su zo su kacacccala shi irin tasu fahimtar .

Amma dai Fawa ta a yanka saniya a fitar da ita dalla-dalla sai da Hausawa musulmi suka zo daga Arewacin Najeriya .sannan suka koya suka kara gogewa a harkar sannan yanayinta a yankin Obubra da ma kuros riba gaba daya wani abu ne mawuyaci saboda halin da dabba ta shiga a yanzu dabba farashin ta yayi hawan da abin malam Sai dai addu’a .saboda tsada.domin wannan dabbar babu ita a kudancin Najeriya daga Arewa ake kawo su sannan idan ka dauko ta fitinar ma’aikata ,da sauran shingayen duba ababen Hawa da ke kan hanya kafin ka iso kuros riba kudin haraji da na gyaran hanya kadai ya ishe ka don haka kafin a zo nan abin ya kure don haka kashi 90 cikin mahauta za ka gan su suna fita cikin sana’ar ba wai mayar da kudin suke yi ba .ana dai yi ne maganin kada a zauna .

Har wa yau ya bayyana dabaryn da suke yi na warware matsala tsakanin su da Fulani masu dabbobi idan sun saya dama rikicin Fawa ita kantsa tsakanin.mahautan  muna  yunkuri na yadda ake Ilmantar da su mahautan musamman a cikin.kowace sana’a jari ne mahimmin abu ne akwai tallafi da gwamnati ta cullo da su take bayarwa 

Muna duba  yiwuwar yadda a kungiyance su nemi tallafi su samu don su kara jari 

Ta fuskar Neman tallafi daga kingoyoyi ko cibiyar bayar da tallafi sarkin Fawan ya ce  Alhamdulillah akwai karamin tsari na tallafi wanda muke gudanar dashi iya daidai karfinmu ,kuma akwai shawarwari da muke ba mahauta tun daga rage yankan 

Kazalika ya bayyana irin.masarar da ya samu tun daga lokacin da ya zama shugaban kungiyar ba shi da ake biyo mahauci azo a kamashi ayi Masa wulaqanci munyi qoqarin shiga tsakiya ba za mu yadda rana daya a zo ayi wa mahauci wulakanci ba alhali kun dade kuna sana’a tare mun yi kokarin dakatar da wannan tsarin shi Bashi yadda ya shiga a hankali idan ma ya taru idan ma za’a biya shi a hankali ake yin ta sannan mun ilmantar da su mahautan su shiga tsari na zamani na taimakon juna .

Ta fuskar kubale kuwa Babban kalunalen su shi ne “Bai wuce na masu karbar rabano ba.”

Karshe ya shawarci mahautan Najeriya da na kuros riba “Kalma daya da za’a fadi ita ce a duk inda mahauci ya samu kansa ya yi taka tsan-tsan da abin da za ka saya ka yanka kasan daga hannun wa ka saya kasan hannun wanda ka saya gudun kar ka fada  kayan da ba su da kyau.”inji shi 

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Sana'o'i

Na fara sana’a ne don na dogara da kaina – Zainab Aqeela Katsina

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Zainab Aqeela Katsina, matashiya mai sana’ar Dambun naman Kaji. Ta shahara sosai a kafofin sada zumunta, wajen tallata sana’arta ta Dambun naman Kaji, kuma tana samun ɗimbim masu saye a wannan kafa ta social media ɗin, a garuruwa daban-daban. Neptune Hausa ta zanta da ita kan wannan sana’a da kuma yadda aka yi ta fara. Hirar ta tavo abubuwa da dama, ga yadda hirar ta kasance;

NEPTUNE HAUSA: Ki gabatar da kanki ga masu karatunmu.

ZAINAB AQEELA: Sunana Zainab Lawal Abdulƙadeer. Ni haifaffiyar Katsina ce. A nan na yi Firamare da Sakandire, yanzu ga shi ina Diploma.

NEPTUNE HAUSA: Ko meye ya ja ra’ayinki kika fara yin sana’a, ganin cewa mafi yawan ‘yan mata suna ɗora nauyin komai nasu ne a iyayensu?

ZAINAB AQEELA: Dalilin da ya sa na fara sana’a shi ne domin na dogara da kaina. Ganin cewa abubuwa sun yiwa iyaye yawa, wani abin ma suna so su yi maka, amma saboda ga ƙannenka, ga kuma wasu yayyenka, waɗanda su ma ba su wuce a yi musu ba. To sai ka ga abubuwan sun yi yawa, ba za ku samu abin da kuke so yadda ya kamata ba. To amma idan kana sana’a, sai ka ga ma kana taimaka wa iyayen da wasu abubuwan. Babban abin da ya sa na fara sana’a, shi ne don na dogara da kaina.

NEPTUNE HAUSA: Ganin cewa akwai sana’o’i da yawa da mata suke yi, me ya sa kika zaɓi ki yi sana’ar Dambun Naman Kaji?

ZAINAB AQEELA: To gaskiya ba ni ne na na zaɓi na yi sana’ar dambun naman kaji ba, dambun naman kaji ne ya zaɓe ni tare da irshadin wani bawan Allah (dariya). Na fara wannan sana’a shekara uku da suka gabata. Asali na fara sana’ar dambun naman kifi ne. Don a lokacin da na fara sana’ar ma ba ni da ko sisi, naira hamsin tana matuƙar burge ni a wancan lokacin. Yadda abin ya faro shi ne, akwai wani bawan Allah da muke mutunci da shi. Mun haɗu da shi ne sanadiyyar auren wani ɗan’uwanmu da aka yi. Shi abokin ango ne. To dai shi ya kawo min kifi, bai ma wuce na ɗari bakwai ba. Shi ne na ce bari na fara sana’a da shi.

To da na yi dambun kifin sai na ɗora a Whatsapp na ce na fara sana’a, shikenan cikin ikon Allah, a haka dai aka yi ta aiko wa har kifi ya ƙare. To akwai wani da yake so na a wancan lokacin, shi ma yana sayan dambun kifin, to shi ne ya bani shawarar na fara dambun naman kaza. To gaskiya a lokacin har na ji haushinsa, saboda yaya za a yi ya ce na fara dambun naman kaza, bayan na kifin ya samu karɓu wa, idan na yi ƙare wa yake nan take. Sai na ce masa bani da jarin da zan fara dambun naman kaza. To sai ya ɗauki naira dubu biyar ya bani, to da ita dai na fara, kuma cikin ikon Allah, shi ma ya karɓu. Yanzu dambun naman kaji na yana shiga jihohi da dama a ƙasar nan.

NEPTUNE HAUSA: Da yake kina ɗora tallan dambun naman kajin naki a soshiyal midiya, ta yaya kike aika wa zuwa jihohi daban-daban?

ZAINAB AQEELA: Batun aika wa jihohi, dole na gode wa al’ummar jihar Kano. Domin gaskiya sune suka fara min ciniki a wata jiha. Daga mutum ya ce yana so, idan ya faɗi adadin da yake so, sai na ɗauka na kai tasha, na rubuta lambarsa, kuma nan da nan sai na ji mutum ya bugo yana cewa saƙonsa ya isa, har ya karɓa. Kuma sai ya ce dambun ya yi daɗi. To wannan yana ƙara min ƙarfin gwiwa. Kowace jiha ta mota nake aika musu, kuma Alhamdulillah, ban taɓa samun matsala a tura wa ɗin ba. Na samu alherai da yawa waɗanda ba zan iya lissafa su ba.

KU KUMA KARANTA: Sana’ar Dinki Na Da Bukatar Sadaukarwa Domin Biyan Bukatun Al’umma

NEPTUNE HAUSA: Ko kin taɓa samun tallafi daga gwamnati ko wata ƙungiya?

ZAINAB AQEELA: Eh to, tsohon gwamnan jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, ya taɓa ba ni kyautar naira dubu ɗari da hamsin (150,000). Yadda abin ya faru shi ne, mun kai masa ziyara ne ƙarƙashin wata ƙungiya ta ƙananan ‘yan kasuwa masu fasaha ta musamman. Dalilin da ya sa ya ba ni kyautar wannan kuɗi shi ne, a lokacin da muka kai masa ziyarar, bayan ya fito, sai kowa ya gabatar da kansa. To da aka zo kaina na ce ina yin sana’ar dambun naman kaji, sai gwamnan ya ce “ina dambun naman yake?” sai na bayar aka miƙa masa. Take a wajen ya buɗe ya fara ci. Kuma wani ikon Allah ni kaɗai ce na je da abin sana’ata a cikinmu.

Gwamna da ya buɗe ya fara ci, sai ya miƙa wa sauran kwamishinoni da sakataren gwamnati. Haka dai aka cinye dambun da na je wajen da shi. Daman dambun naira dubu 18,000 ne. Gwamna ya ce dambun ya yi daɗi. Ya ce “ga daɗi ga araha” shi ne gwamnan ya bani naira dubu ɗari da hamsin (150,000) ya ce a ƙara jari. Amma in ban da wannan ban taɓa samun tallafi daga ko ina ba.

NEPTUNE HAUSA: To wane ƙalubale kike fuskanta a wannan sana’a ta ki?

ZAINAB AQEELA: Babban ƙalubalen da nake fuskanta a wannan sana’a shi ne ‘yan bashi. Sai ka ga mutum babba da girmansa, zai iya saya ya biya kuɗin, amma sai ya ce a aika masa zai turo kuɗin. Amma shiru ba zai turo ba. Kuma ina ganin girmansa ba zan iya hana shi ba. In har na tambaya sau biyu bai ba ni ba, to ba na sake tambaya. To ni wallahi babban ƙalubale na shi ne ‘yan bashi. Da a ce za su fahimci karɓar bashi, a riƙe kuɗin, ruguza mai ƙaramin jari yake, to da sun daina riƙe bashin.

NEPTUNE HAUSA: Wane ƙira kike da shi ga sauran ‘yan’uwanki mata waɗanda ba sa yin sana’a?

ZAINAB AQEELA: Ƙira na ga sauran ‘yan’uwana mata waɗanda ba sa sana’a shi ne, yana da kyau su sani cewa mu mata muna da buƙatu da yawa, ke ce sayan wancan, ke ce sayan wannan. Babu buƙatar sai na bayyana, duk mace ta san da haka. Ba kowane iyaye ba ne suke da ƙarfin da za su sayawa ‘ya’yansu dukkan waɗannan abubuwan. Amma idan kina sana’a kusan komai za ki yiwa kanki, kuma ba ki takurawa kowa ba. Irinsu anko da kayan kwalliya duk za ki yiwa kanki, ba sai kin damu wani da roƙo ba. Kin san roƙo yana zubar da daraja da mutunci, musamman mu mata. Babban abin da sana’a take buƙata shi ne, haƙuri, juriya da addu’a. Musamman addu’ar iyaye.

NEPTUNE HAUSA: Mun gode.

ZAINAB AQEELA: Ni ma nagode.

Continue Reading

'Yansanda

Matar da ake zargi da kisan yarinya a Jos ta shiga hannu

Published

on

Daga Maryam Sulaiman, Abuja

Matar da ake zargi da kisan Yarinya a Jos ta shiga hannuJami’an rundunar ‘yan sandan jihar Filato sun kama Misis Nneamaka Nwachukwu da ake zargi da laifin azabtar da wata yarinya mai suna Margaret Joshua mai shekaru 11wanda hakan yayi sanadiyar mutuwar har lahira.

Rahotanni sun bayyana cewa, wacce aka kashen ‘yar asalin jihar Kebbi ce ta gudu ne saboda rashin tsaron da ke addabar yankin da take, kafin a kai ta wurin wanda ake zargin, wacce ta nemi a taimaka mata.

Bayanai sun nuna cewa yarinyar a lokacin zamanta da wanda ake zargin ba a sanya ta makaranta ba, kuma ana azabtar da ita akai-akai har sai da ta mutu sakamakon hakan. An kuma yi zargin cewa bayan da aka yi mata dukan kawo wuƙa a kwana kwanan nan, an tilasta ta zauna a cikin roba mai dauke da ruwan zafi, hakan yayi sanadiyar ƙonewar gaban ta, kuma ta rasu a asibiti a ranar Litinin 14 ga watan Nuwamba.

Shugaban hukumar kare hakkin bil’adama ta ƙasa reshen jihar Filato, Grace Pam, wadda ofishinta ke bin diddigin lamarin ta shaida wa jaridar Vanguard cewa, bisa la’akari da yawan tabo da raunukan da ke jikin yarinyar dole ne masu kula da ita sun yi ta gallaza mata a lokacin da take tare da su. “Ma’aikatan asibitin sun kira ni akan lamarin a ranar Litinin da ta gabata, inda suka shaida cewa Misis Nneamaka Nwachukwu ta yi wa wata yarinya ‘yar shekara 11 mummunan duka tare da raunata ta.

“Yarinyar tana da tabo da kuna a jikinta, an gaya mana cewa an kai ta asibitin Mandela da ke Kaduna kafin a tura ta zuwa Jos. “Lokacin da wasu ma’aikatanmu suka gana da matar da ake zargin a ofishin ‘yan sanda da ke Vom inda aka tsare ta, ta amsa cewa tana yi mata dukan tsiya kuma ta yi ikirarin cewa yarinyar tana wasa da al’auran ta ne, don haka ta hukunta ta don ta daina.

Ta yi ikirarin cewa ba ta san me yake zuwa mata ba,lokacin da take dukan ta, saboda tana nadaman a duk lokacin da ta doke yarinyan” inji Pam Da take magana game da ƙonewar da ta yi a mazaunin ta, wacce ake zargin ta, ta shaida cewa yarinyar ta faɗa cikin ruwan zafi kuma ta fice daga gidan bayan faruwar lamarin na kusan awa 24.

Sai dai an gano cewa wani ya ga yarinyar da ta ji rauni a kan titi ya kai ta ofishin ‘yan sanda da ke Kaduna Vom. Daga nan sai jami’an tsaro suka kai yarinyar asibiti kafin su kira mai kula da ita Misis Pam ta nuna damuwarta inda take cewa, “ba a dauki matakin kula da yarinyar da ke cikin halin da take ciki ba har na tsawon sa’o’i 24, sai wani ya gan ta ya kai ta. ofishin ‘yan sanda.”

Bayanai sun nuna cewa wannan ba shi ne karon farko da da wadda ake zargin ke cin zarafin yarinyar ba, domin tun da farko ‘yan sanda sun gargaɗe ta da cin zarafin yarinyar tare da neman a mayar da yarinyar ga iyayenta. Matar da ake zargin bata taɓa ganawa da iyayen yarinyar ba, wanda suke jihar Kebbi, amma an ce suna magana da su ta waya.

Sai dai an mayar da shari’ar daga ofishin ‘yan sanda da ke Kaduna zuwa hedikwatar ‘yan sanda da ke Jos yayin da ake ci gaba da bincike. Misis Nwachukwu kafin a kama ta, ta yi aiki a daya daga cikin Cibiyoyin Bincike da ke Vom, karamar Hukumar Jos ta Kudu a Jihar Filato a matsayin Likitan Kwayoyin Halitta.

Continue Reading

Kasuwanci

Gidajen burodi da dama sun rufe a Abuja, saboda tsadar kayan aiki

Published

on

Aƙalla gidajen burodi 40 ne suka rufe shagunansu a babban birnin tarayya Abuja, saboda tsadar kayayyakin aiki, da kuma yawan haraji, tare da ƙarin kudin wutar lantarki da dai sauransu.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa wasu gidajen biredin da suka ziyarta, ba a bude su ba don kasuwanci, saboda tsadar kayan aiki dana haraji da wasu hukumomin gwamnati ke yi.

Wasu daga cikin gidajen burodin da suka rufe sun hada da Abumme bakery Ltd. Lugbe, titin Airports, Hamdala Bakery, Kuje, Harmony Bite Bakery, Karu, Doweey Delight Bakery Ltd, Kubwa. Sauran sun hada da Merit Baker, Mpape, Funez Baker, Orozo, Slyz Bakery, Wuse Zone 2, da sauransu.

Mista Ishaq Abdulraheem, shugaban kungiyar masu yin burodi a Abuja, babban birnin tarayya, ya ce abin na kara tada hankali yadda gidajen burodin da ke Abuja ba za su iya jurewa tsadar kayan da ake aiki dasu ba.

Ya ce akasarin ‘yan kungiyar sun rasa abin dogaro da kai, yayin da ma’aikata suka rasa aikin yi saboda rufewar da aka yi.

Ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta shiga tsakani, ta kuma duba hukumomin gwamnati da ke kawo cikas ga harkokin kasuwancin biredi. Ya bayyana wasu daga cikin hukumomin da suka hada da Hukumar Kula da Magungunan Abinci ta Kasa (NAFDAC), Standard Organisation of Nigeria (SON), National Environmental Standards and Regulations, National Environmental Standards and Regulations, National Enforcement Agency (NESREA).

Wani mai biredi a Abuja, Mista Nuhu Musa na Hamdala Bakery, Kuje, FCT, ya roki gwamnati da ta daidaita ayyukan wadannan hukumomi don rage haraji daban-daban da suke sanyawa masu yin burodi.

Musa ya ce, gidajen biredi da dama na kokawa da rayuwa saboda tsadar sarrafawa. “Muna son gwamnati ta daidaita wadannan hukumomi ta yadda ayyukanmu za su kasance cikin sauki. “Wadannan harajin suna yin mummunar tasiri ga kasuwancinmu har ya kai ga yawancin mu sun rufe. Wannan kuma yana shafar ayyukan yi domin da yawa daga cikin ma’aikatan biredi ba su da aiki a halin yanzu, kuma kun san tasirin hakan ga al’umma; wasu za su koma aikata laifuka,” inji shi.

Musa ya ce, alal misali, NAFDAC za ta zo gidajen burodin su don duba takardun shaida, yayin da SON za ta zo a yi rajistar kayayyakin. “Nawa muke bayarwa don ba da garantin duk waɗannan dubawa da biyan kuɗi,” in ji shi.

Wasu mazauna yankin da suka zanta da NAN sun koka kan tsadar biredi a kasuwar, inda suka jaddada cewa a hankali biredi ya zama abincin masu hannu da shuni. Mista Julius Anthony, wani mazaunin garin ya ce wasu daga cikin biredin da ya saba saya kan Naira 500 kan kowane bulo yanzu sun kai Naira 1,000.

Wata matashiya Aisha Danjuma,  mazauniyar babban birnin ta yi kira ga gwamnati da ta gaggauta shiga tsakani kan tsadar biredi, inda ta kara da cewa “bread abincin talakawa ne kuma ba za a kwace musu ba.” (NAN)

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like