Connect with us

Ilimi

Dan Majalisa Ya Baiwa Yarinyar Da Tazo Ta Biyu A Gasar Alkura’ani Kyautar Mota

Published

on

Daga; Isah Ahmed, Jos.

DAN majalisar wakilai ta tarayya, mai wakilyar Mazabar Lere da ke Jihar Kaduna, Injiniya Ahmed Mannur, ya baiwa wata yarinya ‘yar shekara 13 da haihuwa, mai suna Sumayya Idris da ke zaune a garin Saminaka, kyautar mota kirar Fijo 406, aboda ta zama ta biyu a gasar karatun Alkura’ani mai girma ta Jihar Kaduna da aka gudanar. Ita dai Sumayya Idris, tazo ta biyu ne a gasar karatun Alkura’ani Izu biyu da aka gudanar.

Da yake mika wannan kyautar mota ga Shugaban kwamitin shirya gasar karatun Alkura’ani na Karamar Hukumar Lere kuma Limamin masallacin Juma’a na Kamfa da ke garin Saminaka Imam Aminu Muhammad Aminu da iyayen wannan yarinya, a garin Saminaka, Mai taimakawa Dan majalisar wakilan na musamman Barista Nuhu A.Nuhu ya bayyana cewa, Dan majalisar wakilai ta tarayya Injiniya Ahmed Mannur ne, ya wakilta shi, don ya zo ya mikawa Sumayya Idris alkawarin da ya yi, na kyautar mota. Saboda nasarar da ta samu na kasancewa ta biyu a gasar karatun Alkura’ani ta jihar Kaduna a matakin Izu na biyu.

“Ganin wannan kokari da tayi, yasa ya yi mata alkawarin kyautar mota kirar fijo 406 ,kuma yau gashi ya aiko da wannan alkawari da ya yi. Muna kira ga yara matasa na wannan mazaba, su kara kokari domin wannan kyauta da ya yiwa wannan yarinya, ya fara ne ga dukkan matasan wannan yanki, musamman masu kokari”.

Da yake jawabi Shugaban kwamitin shirya gasar karatun Alkura’ani na Karamar Hukumar Lere, Imam Aminu Muhammad Aminu ya bayyana matukar farin cikin su, da godiyarsu ga wannan Dan majalisa.

Ya ce wannan karramawa da wannan dan majalisa ya yi masu, wani babban girmama ne, kuma duk mutumin da ya girmama ma’abucin ilmi, ya girmama ilmin ne.

Ya yi kira ga ‘yan majalisa da sauran masu hanu da shuni, su yi koyi da wannan dan majalisa.

Da take zantawa da wakilinmu, Sumayya Idris ta bayyana cewa gaskiya
lokacin da aka ce tazo ta biyu a wannan gasa, sai taji kamar tana mafarki ne.

Ta ce tayi farin ciki da wannan kyautar mota da aka bata, don haka tayi godiya tare da rokon Allah ya sakawa, wannan dan majalisa da alheri.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ilimi

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Published

on

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Daga Idris Umar, Zariya

Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.

Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.

Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.

KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.

A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.

Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.

Continue Reading

Ilimi

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Published

on

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa - Dauda Lawal 

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal

Daga Idris UMAR, Zariya

Gwamna Dauda Lawal ya halarci taron yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu na Jami’ar tarayya, wanda ya gudana a filin taro na Jami’ar da ke Gusau a cikin satin da ya gabata

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya shelanta bayar da gurbin karatu ga duk wanda ya zo na ɗaya a Jami’ar.

Cikin jawabinsa a wurin taron, Gwamnan ya yaba wa shugabannin Jami’ar game da yadda suka iya ririta ɗan abin da suke da shi, duk da ɗimbin ƙalubalen da suke fuskanta.

Ya ce, “Ina matuƙar farin cikin kasancewa da ku yau a wannan bikin yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu a wannan jajirtacciyar Jami’a, Jami’ar gwamnatin tarayya ta Gusau.

Ina taya jami’ar nan murnar samun wannan nasara, duk kuwa da matsalolin da suke fuskanta tun lokacin da aka kafa ta. Ina kuma yaba wa iyaye da ɗalibai bisa sadaukarwar da suka nuna har zuwa wannan matsayi.

Muna sa ran samun makoma mai kyau kuma mai albarka duk da tarin ƙalubalen da muke fuskanta a matsayinmu na jiha kuma al’umma.

Muna yin addu’a kuma muna aiki ba dare ba rana don samar da makoma mai kyau. Duk waɗannan matsaloli za su wuce da izinin Allah Maɗaukakin Sarki.”

Gwamnan ya yi ƙarin haske kan ƙoƙarin gwamnatinsa na gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara bayan kafa dokar ta-ɓaci a bara.

“A matsayinmu na gwamnati, mun ƙuduri aniyar ilimantar da duk ’ya’yan Zamfara. Ilimi shi ne ginshiƙin da ke haskaka ruyuwar ɗan adam.

“Mun ware maƙudan kuɗaɗe ga ɓangaren ilimi a cikin kasafin kuɗinmu na 2024 kuma muna fatan za mu kai ga babban matsayi a 2025, 2026, da 2027. Muna fatan cimma kashi 25 zuwa 30 na haɓaka tsarin ilimi.

Tare da samar da ingantaccen tsari a fannin da sarrafa albarkatun da ya ƙunsa, muna da ƙwarin gwiwar cewa za mu farfaɗo da ababen more rayuwa, ɗaukar ƙwararrun malamai, horarwa da sake horar da waɗanda ake da su.

“Za kuma mu ƙara yawan masu karatu a makarantun firamare da na gaba da firamare ta hanyar wayar da kan jama’a da samar da ingantattun wuraren koyo da koyarwa. Ilimi kyauta ne, kuma muna fatan ya zama wajibi ga kowa.

“Mun kuma yi wa manyan makarantunmu da ke jihar kason kuɗi mai yawa don fara aikin gyara su zuwa matakai masu inganci.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

A karon farko Jami’ar Jihar Zamfara na shirye-shiryen amincewa da shirin Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa.

Mun umurci ’yan kwangilar da gwamnatin da ta shuɗe ta tilastawa barin wuraren aiki da su koma bakin aiki, kuma muna fatan nan da watanni masu zuwa, rukunin dindindin na jami’ar zai fara aiki. A lokaci guda, NUC za ta amince ga duk kwasa-kwasai.

“Mun karɓi mulki a jihar da gwamnati ta ƙi biyan kuɗaɗen jarrabawar WEAC da NECO har na biliyoyin Naira fiye da shekaru uku.

Dole muka yi shiri na musamman da hukumomin, kuma tun daga lokacin an fara biyan kuɗi a kan kari kuma za a kammala su a kan lokaci.

“A cikin ƙarancin albarkatunmu, za mu ci gaba da bayar da taimako ga jami’a. Burinmu shi ne mu ƙara haɓaka ilimi a jiharmu ta yadda za a samu damarmaki ga ɗaukacin matasanmu da za a horar da su don kai ga ƙololuwar da ilimi ke samarwa.”

Continue Reading

Ilimi

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Published

on

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Jami’o’in ƙasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO.

Shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa (NECO), Farfesa Ibrahim Wushishi, ya ce Jami’ar Lead da Jami’ar Birmingham City da ke kasar Birtaniya sun tuntubi hukumar  kan jarabawar da take shiryawa.

Ya ce  jami’o’in sun fara tunanin bai wa daliban Najeriya gurbin karatu da sakamakon jarabawarsu ta NECO.

KU KUMA KARANTA: JAMB zata duba yiwuwar amfani da wayoyin hanu a jarabawar UTME

A fahimtarsa, hakan na nuni da  amincewa da ingancin sakamakon jarabawar NECO ne a idanun manyan jami’o’in ciki da wajen Najeriya.

Farfesa Wushishi ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa da ’yan jarida a Abuja ranar Laraba.

Ya ce NECO ta cika sharudan Jami’ar Birmingham City, kuma a halin yanzu suna aiki tukuru kan ganin sun sami cika sharudan jami’ar Lead.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like