Connect with us

Labari

An Gudanar Da Taron Horas Da Yan Jaridun Kaduna Kan Yanayin Yada Labaran Rikice-Rikice

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A WANI yunƙuri na karin samun zaman lafiya a bisa aikin jarida da bayar da sahihan rahotanni domin kawar da duk wata tarzoma, wata kungiya mai zaman kanta, Mercy Corps (MC) tare da haɗin gwiwar cibiyar sasantawa tsakanin addinai (IMC), reshen Jihar Kaduna sun horar da ‘yan Jaridu arba’in (40) kan yadda za a bayar rahoton rikice-rikice a Kaduna.

Taron horon wanda ya a cibiyar yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kaduna, ya kasance na yini biyu ne domin gina kwarin gwiwar ga yan Jaridu ta yadda za su rika bayar da rahoton yadda ake tada zaune tsaye ba tare da tada hankali ba.

A jawabinsa na maraba, Mista Godwin Okoko wanda ya wakilci darakta na kasa, MC Ndubisi Anyanwu ya bayyana cewa kungiyar wata kungiya ce ta duniya da ke kokarin samar da makoma mai kyau ta yadda kowa zai samu ci gaba.

Ya yi nuni da cewa, rawar da kafafen yada labarai ke takawa wajen samar da zaman lafiya da ci gaba ba za a iya misilta shi ba, don haka ake da bukatar ba da horon kara inganta karfin gwiwar ga yan Jaridun.

Ya bukaci mahalarta taron da su mai da hankali kan horarwa da aiwatar da ilimin da suka koya a cikin rahotanninsu.

Tun da farko a nata jawabin, shugabar cibiyar kungiyar ‘yan Jaridun (NUJ), reshen Jihar Kaduna, Hajiya Asma’u Halilu, ta bayyana cewa sana’ar aikin jarida na bukatar a rika ba da horo akai-akai domin inganta kwarewar kwararrun ‘yan Jaridu don gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Ta ce, “batun horon na ranar ya dace, duba da yadda a ‘yan kwanakin nan aka kama wasu ‘yan jarida ko kuma daure su a yayin gudanar da ayyukansu.

“Da yawa daga cikinsu sun kasance wadanda abin ya shafa saboda rashin sanin ya kamata a kan rahoton la’akari da rikice-rikice.

“Kyakkyawan aikin jarida na bukatar mu gudanar da tantancewa yayin da ake fama da rikici don fahimtar bangarorin da abin ya shafa da kuma rawar da suke takawa a lamarin kafin mu watsa wani bayani,” in ji ta.

Hajiya Halilu ta kara da cewa kafafen yada labarai su ne matakin iko na hudu a duniya kuma madubin al’umma inda ta bukaci kwararrun da su rika bin ka’idojin sana’ar yayin da suke bayar da rahotannin rikici.

Hakazalika, Malam Jamilu Yahaya Jega, Daraktan Shiyya na Hukumar Yada Labarai ta Kasa (NBC) ya bayyana cewa akwai dokoki da tsare-tsare da ke tafiyar da rahoton rikice-rikice.

Yahaya wanda ya yi magana kan tsari da manufofi na hukumar don magance rahotannin rikice-rikice, ya bayyana cewa ana sa ran manema labarai su gabatar da labarai da sharhi kan rikici ko gaggawa cikin kwarewa.

Ya ce “dangane da wannan makala da aka gudanar, ina saran duk wanda yazo wannan taro ya karu don ba mu su har ni kaina na karu saboda akwai jami’ai da dama sun yi bayanai wanda akasarin mutanen da ba su da kwarewa sun karu kuma an gudanar da shi ne don inganta aikin Jarida.

“Kuma abin da na yi magana a kai shi ne a kiyaye tsabtace harshe amma mutane da dama su kan yi kuskure, musamman ma Kafafen yada labarai na wannan zamani domin zamani ne wanda yake tattare da kaulubale, amma mutane da dama su kan yi ko oho da wannan kalubalen sai fadi abinda aka gardama a wannan zamani.”

“To Dokoki suna nan, wanda ya kamata a kiyaye harshen su domin a tsabtace irin kalaman da ale yadawa saboda bai halattaba ga dan Jarida ya bada damar a ci zarafin wani, bai kamata ba a furta kalamai batanci ga wani, bai kamata ba a fadi kalma wacce za ta tunzura Jama’a, bai halattaba ga dan Jarida ya bada dama a riki amfani da kafar yada labarai domin isar da sako wacce za ta kawo rudani a cikin Jama’a.

Mahalarta taron sun nuna jin dadinsu ga kungiyoyin biyu da kuma kungiyar NUJ da suka shirya horon inda suka ce ya dace kuma ya kamaci a ci gaba da gudanar da irin wannan horaswan izuwa lokaci zuwa lokaci.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Buhari ya taya ‘yan jarida murnar zagayowar ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like