Connect with us

Labari

An Buƙaci Al’ummar Musulmi Su Koma Ga Gwamnatin Allah Don Samun Saukin Rayuwa

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

AYAYIN da al’ummar Musulmi a fadin duniya ke bikin Sallah Karama na watan Azumin Ramadana, an buƙaci al’umma da mayar da al’amuransu zuwa ga Allah domin samun sauki da mafita daga cikin halin kangi da kuncin rayuwar da suke fuskanta musamman a kasar Najeriya.

Da yake gabatar hudubarsa na Sallar Idin bana a filin Makarantar Sakandaren Gwamnati dake Rigasa Kaduna, Imam Rabi’u Ali Tanko, ya bayyana cewa halin da al’umma suka tsinci kansu a yanzu na rashin tsaro da tsananin rayuwa na da bukatar al’umma su koma ga Allah don neman dauki da samun tsira daga wajen Allah madaukaki.

Limamin ya kara da cewa, babu shakka da akwai bukatar mutane su koma ga Allah musamman a yanzu da al’amarin garkuwa da mutane ya ci karfin al’umma dukda Gwamnati da Jami’an tsaro na iya bakin kokarinsu, toh amma al’amarin na da bukatar yin addu’o’in na neman kariya daga wajen Ubangiji.

Ya ce “mu tuna a rana ta Idin nan, akwai wadansu wadanda yan Uwansu suna can a cikin daji a hannun masu garkuwa da mutane, don haka dole mu taya su da addu’a, sannan su kuma masu yin irin wannan aikin ayi musu addu’ar Allah Ya shiryesu, Ya taba zukatansu, Yasa su gane kimar rayuwar dan Adam don ka da su keta wannan haddin idan suna so su gyara zamantakewarsu tsakaninsu da Ubangiji kuma lahirarsu tayi kyau.

Hakazalika Imam Rabi’u Ali, ya kara da cewa hudubar ta kuma yi bayani a kan zamantakewa tsakanin al’umma wanda ke nuni bisa irin alakar dake tsakani iyalai wanda suka hada tsakanin Ya’ya da iyayensu domin neman Aljannarsu, yanayin zamantakewa tsakanin mata da miji da sauran al’umma domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma.

Acewarsa, rashin nuna so da kauna a tsakanin al’umma ne musabbabin duk wata musibar da al’umma ke ciki wacce ta haifar duk wasu tashe-tashen hankali da matsalolin da ake fuskanta, don haka ya zama wajibi al’umma su kaunaci juna, tare da nuna soyayya gaskiya na tsakani da Allah a tsakaninsu domin samun duk wata sauki da mafitar da ake bukata.

Da yake tsokaci kan al’amuran, Sarkin Sabon Garin Rigasa, Kaduna Alhaji Muhammad Jibril, ya bayyana farin ciki bisa samun damar kammala Azumin da a bana aka yi talatin, kana da sake ganin zagayowar wannan rana ta farin ciki da ake bukatar al’umma su nuna farin ciki ta hanyar ziyartar yan Uwansu, kana da yi wa junansu kyakkyawar fata.

Sarkin a matsayinsa na uban kasa na wannan yankin, ya kara da Jan hankalin al’umma musamman matasa da su yi kokarin kiyaye yin duk wasu abubuwan da suka sabawa karantar Addinin Islama domin duk Musulmi ya kamata yasan cewa shi Musulmi ne, kana ya shawarci al’umma da su ci gaba da yin sauran ibadodi kamar yadda Allah Ya ce.

A Karshe, Sarki Muhammad Jibril, ya yi godiya ga Allah bisa ga wannan ni’imar kana da miki gaisuwa ga Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, mai Martaba Sarkin Zazzau Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, Dan Galadiman Zazzau da sauran Sarakuna da daukacin al’ummar Musulmi baki daya musamman na Sabon Garin Gundumar Rigasa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like