Connect with us

Siyasa

Zamfara: Yan Takarar Gwamna 3 Sun Bukaci Soke Zaben Fidda Gwani Na Jam’iyyar PDP

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WASU yan takarar Kujerar Gwamnan Jihar Zamfara akalla mutane uku (3) wadanda suka hada da Ibrahim Shehu Gusau, Wadatau Madawaki da Aliyu Hafiz Muhammad sun garzaya kotu domin kalubalantar tsayar da Dauda Lawal Dare a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaben fidda gwani na Jam’iyyar ta PDP a Jihar.

Daya Dan takarar Ibrahim Shehu Gusau, a ta bakin babban lauyansa, Barista Ibrahim Ali Abubakar, a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a Kaduna, ya bayyana cewa wanda yake karewa yana gaban babbar kotun Zamfara yana neman a soke zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar PDP daya gudana a ranar 25 ga watan Mayu.

Da yake karin bayani, Barr. Abubakar ya bayyana cewa rashin bin ka’ida, rashin daidaito, zamba, karya kundin tsarin mulkin jam’iyya, tanade-tanaden ayyukan zabe da dai sauran su a matsayin dalilan neman soke aikin.

“Muna da kwakkwarar hujja kuma mun gabatar da shaidun da ke nuna cewa atisayen da Adamu Maina Waziri ya yi, ya kasance da kura-kurai da dama ba tare da la’akari da tanade-tanaden da jam’iyyar ta yi na gudanar da zaben fidda gwani ba.

“Sai dai abin da Adamu Maina Waziri wanda shi ne shugaban kwamitin zaben ya yi, ya kasance cikakkiyar gadar tanade-tanaden kundin tsarin mulki, da dokokin zaben kasar nan na 2022 da sauransu.

“Saboda haka addu’armu ita ce, neman soke zaben gaba dayansa da umarnin kotu domin a sake yin wani sabon zaben a karkashin kulawar wasu marasa son zuciya wanda zai bai wa duk masu son tsayawa takara dama daidai da yadda jam’iyya da kasa suka tanadi dokoki da ka’idojin da ke jagorantar gudanar da zaben fidda gwanin” in ji Barista Ibrahim.

Idan dai za a iya tunawa Adamu Maina Waziri wanda shi ne Shugaban Kwamitin Zaben Gwamnan Jihar Zamfara na PDP ya bayyana Dauda Lawal Dare a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan Mayu.

Halin da wasu ‘yan takara uku; Wadatau Madawaki, Aliyu Hafiz Muhammad da Injiniya Ibrahim Shehu Gusau ya ce an tafka magudi da rashin bin ka’ida, inda ya ce aikin ya sabawa ka’idojin jam’iyyar da kuma dokokin zabe.

Sai dai wadanda ake tuhumar ba su halarci zaman farko na karar da mai shari’a Aminu Bappa na babbar kotun tarayya da ke Gusau ya jagoranta ba.

Mai shari’a Bappa yayin da ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 8 ga watan Yuli saboda rashin halartar wadanda ake kara da kuma lauyansu, ya umurci wadanda ake kara da su mayar da martani cikin kwanaki 30 da ikirari na mai kara Ibrahim Shehu Gusau.

Wadanda ake tuhumar sune; Adamu Maina Waziri, shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Zamfara, da Kanal Bala Mande (rtd). Haka kuma da hukumar Zabe (INEC) tare da Dauda Lawal Dare wanda aka bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like