Connect with us

Labari

Za Mu Ci Gaba Da Bunkasa Harkar Noma A Najeriya – CBN

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

AN bayyana Babban Bankin Najeriya, (CBN) a matsayin wanda zai kara bunkasa harkokin Noma da ci gaban kasa baki daya.

Da yake zantawa da manema labarai, Wakilin babban Bankin Najeriya Mista Philip Yila Yusif, ne ya bayyana hakan
a wajen babban taron kaddamar da Dalar Masarar da aka karba a hannun manoman da Bankin ya ba rancen yin Noma da aka yi a Kaduna.

Philip Yila Yusif, wanda ya wakilci Gwamnan babban Bankin Najeriya Godwin Emefele, a wajen kaddamar da Dalar Masara karo na biyu da aka yi ta hanyar hadin Gwiwa tsakanin babban Bankin Najeriya da kungiyar masu kokarin Farfado da Noman Masara ta MAAN, ya ce daya daga cikin dalilan da ya sa ake yin wannan Dalar Masara shi ne domin a tabbatarwa da Jama’a cewa babban Bankin kasa zata iya jagoranci wajen dawowa da irin Dalar kayan amfanin Gona da aka Sani a can baya

“Mun yi Dalar Shinkafa kuma yau ga shi an yi Dalar Masara wanda ke nuni da cewa hakika Manoman Masara na kokari wajen yin Noma ta hanyar yin amfani da kayan Noman da suke karba daga babban Bankin Najeriya bisa tsarin saboda haka wannan abin farin ciki ne kwarai.

“Kuma dukkan wannan Masarar da muka tara za mu Sayarwa masu masana’antun yin abincin Kaji da kamfanonin da ke sarrafa Masara domin amfanin al’umma ta yadda za a samu saukin farashi a kasuwa, kuma a bisa binciken da muke yi ana samun saukin farashi kwarai a Kasuwannin sayar da amfanin Gona, musamman ga masu yin abincin Kaji sun tabbatar da samun sauki kwarai.

Ya kuma bayyana kungiyar masu kokarin samar da Masara ta kasa a matsayin muhimman mutanen da babban Bankin Najeriya ke alfahari da su wajen kokarin biyan abin da aka ba su da kayan Noman da suka Noma, domin mu na yin aiki tare da su a tsawon shekaru biyar da suka gabata.

Don haka zan iya gaya maka cewa su na biyan abin da aka ba su, sai kuma akwai wadansu kamfanonin Noma da suma suke kokari irin kamfanin “AFEX” ko a Daminar Bara da ta gabata sun biya kashi dari bisa dari na abin da aka ba su a daminar Bara.

“Zan yi amfani da abin da Gwamnan Babban Bankin Najeriya ya ce ba ma son tsabar kudi, mu na son kayan amfanin Gonar da aka Noma ne kawai. Kuma muna ajiye shi ne a wuri mai kayau da zarar an samu hauhawar farashin amfanin Gona sai babban banki ya fito da shi a sayar wanda hakan na taimakawa kwarai a samu ragowar farashin kayan amfanin Gona a duk fadin kasa baki daya.

Ana nan ana aikin Farfado da tsarin yin musaya da amfanin Gona da aka samu, kuma kafin nan da tsakiyar wannan shekarar za a ga cewa wannan bangaren da ake kokarin farfadowa da shi zai ci gaba da aiwatar da aiki kamar yadda ya dace, ta yadda za a samu biyan bukata ta hanyar kara bunkasa harkokin Noma a Najeriya.

Philips, ya ci gaba da cewa idan kamfani na bukatar ayi hulda da ita, babban Banki zata duba bukatar farko sannan da karfin kamfani shin ya kai mai samar da metric ton 120 kuma yaya tazara a kasuwa ka tu na fa babban aikin Bankin Najeriya shi ne ya dai- daita farashi ba mu son farashi ya kasa tsaya wa wuri daya don haka sai a duba aga me za a iya yi domin ba a son a ba su da yawa ya zama ya yi yawa domin ya na iya shafar kasuwa shi yasa ake kokarin tsayar da farashi wuri daya.

“Muna bayar da kudi domin samar da kayan Noma sama da guda 21, don haka muka fi Sanya muhimmanci ga wasu kwarai kamar Masara, Auduga da sauransu da nufin sama masu Darajar da ta dace, don haka manufar da ta Sanya ake samar da wannan Dalar Masara shi ne a nunawa duk duniya cewa Gwamnati na samun abin da take bayarwa ga manoma kuma a kara masu kwarin Gwiwar yin Noman.

Don haka abin da ake gani a yanzu Bankin zai dauki ragama kuma da abin da ake gani a yanzu da kuma na dimbin Masarar da ke a wuraren ajiya daban daban.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like