Connect with us

Siyasa

Kaduna 2023: Dattijo Ya Fara Rangadin Ganawa Da Shugabannin Jam’iyyar APC

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

BIYO bayan sanarwar bayyana ra’ayin tsayawa takarar neman Gwamnan Jihar Kaduna da Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo) ya yi a ranar talata, Dan takarar ya fara rangadin kwana biyu a kananan hukumomin Jihar domin ganawa da shugabannin Jam’iyyar APC da manyan masu ruwa da tsaki a unguwanni da kananan hukumomi domin neman goyon bayansu gabanin zaben fidda gwani na Jam’iyyar.

Tuni Dattijo da tawagarsa sun ziyarci kananan hukumomi bakwai dake cikin Shiyya ta daya wadanda suka hada da kananan hukumomin Lere, Kubau, Ikara da Soba a ranar Laraba.

Kuma a rana ta biyu, tawagar ta zagaya kananan hukumomin Sabon Gari, Kudan da Makarfi, a ranar Alhamis. Idan dai za a iya tunawa, a baya Dattijo ya gana da masu ruwa da tsaki daga karamar hukumar Zariya.

Yayin da tawagar Dattijo a Lere ta fara da ziyarar mai martaba Sarkin Lere, Injiniya Suleiman Umar Lere da Mai Martaba Sarkin Saminaka, Honarabul Muhammadu Sani, dukkansu sun yi masa addu’o’i da fatan alheri.

Da yake jawabi ga dimbin Jama’ar da suka tarbesu, Muhammad Sani Dattijo ya mika godiyarsa ga ‘ya’yan Jam’iyyar bisa goyon bayan da suke baiwa gwamnatin APC mai ci na tsawon shekaru.

Dattijo ya bukace al’ummar da su mara masa goyon baya a kan burinsa na ganin cewa ya kara karfafawa a kan nasarorin ayyukan da Gwamna Nasir El-Rufai ya ke yi.

Dattijo, ya kuma shawarci ‘ya’yan Jam’iyyar da su kasance masu hadin kai da biyayya ga Jam’iyyar da Gwamna Nasir El-Rufai.

A cewar Dattijo, akidar Jam’iyyar ta na sama kowa kuma fiye da muradin su, don haka dole ne kowane mamba ya kasance mai biyayya ga Jam’iyyar a karkashin jagorancin shugabansu Malam Nasir El-Rufai.

Shugabanni masu kishin Jam’iyyar da shugabannin Jam’iyyar da masu ruwa da tsaki daga matakin kananan hukumomi da na Unguwa a fadin kananan hukumomi 7 sun bayyana goyon bayansu ga muradin Muhammad Sani Dattijo.

Za a ci gaba da rangadin ne a mako mai zuwa tare da kai irin wannan ziyarar a wasu kananan hukumomin dake shiyyar ta biyu da ta uku na jihar Kaduna.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like