Connect with us

Siyasa

Zaben 2023: Dattijo Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Ayyukan El-Rufai Idan Aka Zabe Shi

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A YAYIN da guguwar zaben ke kara karatowa domin zaben wanda zai maye gurbin Gwamna Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i a gidan Sir Kashim Ibrahim Kaduna, wani dan takarar Jam’iyyar All Progressive Congress (APC), Mohammed Sani Dattijo, ya kaddamar da wani shiri mai dauke da tsari shida yayin tsayawa takara a Jihar domin tunkarar babban zaben shekarar 2023.

Dattijo wanda ya jagoranci dimbin magoya bayansa zuwa Sakatariyar Jam’iyyar APC a ranar Talata, ya yi alkawarin ci gaba da kyawawan ayyukan da Gwamna Malam Nasir El-Rufa’i ke yi idan aka zabe shi.

Dan takarar Gwamnan wanda ya kasance tsohon shugaban ma’aikata (CoS) ga Gwamna El-Rufa’i kuma kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare, ya nemi goyon bayan shugabannin Jam’iyyar gabanin zaben fidda gwani na Jam’iyyar domin fitowa a matsayin mai rike da tutar Jam’iyyar.

Jim kadan bayan kammala ganawar da shugabannin Jam’iyyar a sakatariyar APC na Jihar, Dattijo ya yi jawabi ga manema labarai inda ya fitar ajandarsa guda shida wanda idan aka zabe shi a matsayin Gwamnan Jihar zai aiwatar.

A cewarsa, tsarin nasa su ne, “Tabbatar da ci gaba da gina Jihar Kaduna domin tabbatar da tsaro da saka hannun jari ga Jama’ar, kana da amfani da sabbin fasahohi don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin mutanen Jihar ta Kaduna.

“Samun canji na haɗa tattalin arzikin yankunan karkara zuwa Noma da Ƙarfafa samar da ma’adanai masu daraja domin samar da yanayi mai aminci da tsaro don bunƙasa rayuwa.

“Karfafa samar da Kayayyakin Gari domin Fadada Shirin Sabunta Birane na Kaduna domin mayar da Jihar wuri mai samar da damammakin tattalin arziki ga kowa.

“Gina Kaduna mafi kyau da ci gaban fasaha da daidaita tsarin mulki, yin amfani da fasaha don sanya Jihar Kaduna ta zama cikin tsara kuma shiri don tattalin arzikin kamfanoni masu zaman kansu.

“Saka hannun jari a cikin mutane – Samar da yanayi mai kyau kuma mai haɗaka ga jama’ar mu masu juriya ta hanyar zuba jari a kiwon lafiya, ilimi, ci gaban matasa da ayyukan yi.

“Jan hankalin abokan hulda na gida da na waje na kasa da kasa don samun Ci gaba. Yin aiki tare da abokan haɗin gwiwar ci gaba a duk faɗin duniya don ƙaddamar da nasarar ci gaba mai dorewa da kuma tabbatar da cewa ba a bar mafi yawan Jama’a a baya ba.

“Babban burina shi ne in mayar da Kaduna Jihar da za ta kasance mai tsaro, mai aiki ga kowa da kowa, samar da yanayi mai kyau na damammaki ta yadda dukkan mazaunanmu za su ci gaba.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like