Connect with us

Wasanni

‘Yan wasan Man City bakwai sun tafi jinya

Published

on

Rahotanni suna nuna cewa kusan ‘yan wasa bakwai na Man City ba za su samu damar buga wasan da ke gaban ƙungiyar ba na ranar Lahadi mai zuwa, wato wasansu da Arsenal a Gasar Firimiya.

Arsenal ce dai ke jan ragamar teburin gasar Firimiya, inda take saman Liverpool wadda duk da cewa su biyun suna da maki 64, bambancin yawan kwallaye ya sa ta shige gabanta.

Kasancewar Man City na da maki 63, a mataki na uku, ya sa wasan nasu da Arsenal yana da matukar muhimmanci, domin kuwa zai iya kai su ga hayewa saman teburin idan har ita ma Liverpool ba ta yi nasara ba.

Sai dai kash, ƙungiyar da ke rike da kofin Firimiya na bara, tana fuskantar babban ƙalubalen yiwuwar rashin manyan ‘yan wasanta da za su taimaka mata ta yi galabata.

Jerin dakarun ‘yan wasan Man City da ake tsoron ganinsu a wasan na gaba sakamakon tafiya jinya sun hada da Kevin De Bruyne, da John Stones, da Kyle Walker, da Manuel Akanji.

“Waɗannan ‘yan wasa sun samu raunuka ne a wasannin da suka buga wa kasashensu na asali, a jerin wasannin sada zumunta na ƙasa-da-ƙasa da aka kwashe makonnin ƙarshen watan Maris ana gudanarwa.

“Yawancin ‘yan wasan ‘yan baya ne da ke taimakon kungiyar tsaron baya. Ammma kuma akwai Kevin De Bruyne wanda zai zama babban rashi ga karfin ƙungiyar na kai hari.

Sannan kuma akwai tsoron rashin wasu manyan ‘yan wasan kamar Jack Grealish da Matheus Nunes wanda ba dole su iya dawowa buga wasa ba a ranar ta Lahadi.

Shi ma mai tsaron raga, Ederson zai iya rasa wasan na gaba, sakamakon cigaba da jinyar da ya fara bayan da aka cire shi a wasansu da Liverpool saboda jin rauni, tun makonnin baya.

KU KUMA KARANTA: Man United ba za ta sayo Bellingham na Real Madrid ba

Nunes wanda ɗan Portugal ne, ya samu rauni inda aka cire shi a wasan sada zumunta da ya buga wa kasar tasa. Shi kuwa De Bruyne da ma yana fama da ciwon ciki ne.

A tarihin karawar Man City da Arsenal na baya-bayan nan, City ce ta fi samun galaba, musamman a wasannin da suka buga a gidanta da ke filin wasa na Etihad. Amma dai a wasansu na farko na kakar bana, Arsenal ce ta doke City da ci 1-0.

Wannan ne ya sa dole koci Guardiola ya sha jinin jukinsa yayin zuwa wannan wasa ba tare da dakarun ‘yan wasansa ba, musamman ganin cewa akwai wasanni gasar FA da Chelsea, da kuma na Zakarun Turai da Real Madrid.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Wasanni

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Published

on

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Ɗan wasan gaba na Inter Miami Lionel Messi ya jagoranci ƙasarsa Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America inda ta doke Canada da ci 2-0.

Messi mai shekaru 37 ya zura ƙwallo a minti shida da komawa daga hutun rabin lokaci.

Ɗan wasan Manchester City Julian Alvarez ne ya baiwa ƙasar wadda ke rike da kofin duniya damar samun wannan nasara bayan ƙwallon kusa da Rodrigo de Paul na Atletico Madrid ya buga.

Wannan dai shi ne karo na shida a karawa takwas da Argentina wacce ta lashe kofin Copa America sau 15 ta kai matakin wasan ƙarshe.

Wasan ƙarshen da Argentina za ta kara da Uruguay ko Colombia, zai kasance wasa na ƙarshe da Angel di Maria zai buga wa ƙasar kafin ya yi ritaya daga buga wasa sannan kuma akwai shakku kan makomar Messi.

”Za mu ji daɗin yanayin da muke ciki a matsayinmu na ƙasa kuma ƙungiya. Ba abu ba ne mai sauƙi kasancewarmu a matakin wasan ƙarshe domin sake fafatawa don zama zakara,” kamar yadda Messi ya shaida wa kafar TYC Sports.

Manajan Argentina Lionel Scaloni ya ce zai yi aiki don shawo kan Di Maria da Messi su ci gaba da buga wasannin ƙasa da ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Farin cikina ya dawo bayan komawa Inter Miami – Messi

“Yanayin Leo (Messi), yana kama da Angel,” in ji Scaloni.

”Dole ne mu bar shi ya yi abin da yake so, don ba za mu taɓa zama waɗanda za su rufe masa ƙofa ba, zai iya zama tare da tawagarmu har tsawon lokacin da yake so. kuma idan yana so ya yi ritaya kuma ya dawo ya kasancewa tare da mu, za mu yi farin cikin hakan.”

Jacob Shaffelburg, ɗan wasan ƙungiyar MLS Nashville ne ya ɓarar da mafi kyawun damar da Canada ta samu a farkon wasanta da Argentina.

Kasar Canada wacce ke matsayi na 48 a duniya, ta yi waje da ƙwallon da Alvarez ya zura a ragarta kana ya bai wa Argentina damar samun gurbi na gaba a wasan.

Duk da shan kayen Canada, tawagar ta yi rawar gani fiye da yadda ake zato a fafatawar da suka yi a gasar Copa America.

A ranar Lahadi ne tawagar Jesse Marsch wacce za ta ɗauki nauyin gasar cin kofin duniya ta 2026 tare da Mexico da Amurka, za su kara da wadanda suka sha kashi daga sauran wasan kusa da na ƙarshe a wasan neman matsayi na uku.

Continue Reading

Nishadi

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Published

on

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Jarumar TikTok, Sayyada Sadiya Haruna ta sake amarcewa a ranar Juma’a watanni kaɗan da mutuwar aurenta da jarumin TikTok Al Ameen G-Fresh.

A wani kati da ta wallafa a shafinta na Instagram, Sadiya ta bayyana sunan angon nata a matsayin Hon. Babagana Audu Grema.

An daura auren ne da misalin ƙarfe ɗaya bayan sallar Juma’a kamar yadda katin ya nuna a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin tarayya ta bai wa Rahama Sadau muƙami

Auren na zuwa mako guda bayan da jarumar ta TikTok ta bayyana a shirin tattaunawa na jarumar Kannywood Hadiza Gabon “Gabon Talk Show” inda Sadiya ta caccaki G-Fresh tare da bayyana matsalolin da suka kai ga mutuwar aurenta da shi.

Auren har ila yau na zuwa ne kwana guda bayan da shirin na Gabon ya watsa tattaunawar mayar da martani da G-Fresh inda shi ma ya yi ta sukar tsohuwar matar tasa – mafi aksarin lokuta a kaikaice.

Continue Reading

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like