Connect with us

Wasanni

Man United ba za ta sayo Bellingham na Real Madrid ba

Published

on

Attajirin nan da ke cikin mamallakan ƙungiyar Manchester United, Jim Ratcliffe, ya bayyana cewa ba zai nemi ƙungiyar ta sayo gwanayen ‘yan wasa irinsu Jude Bellingham, ɗan asalin Ingila wanda ke buga wasa a Real Madrid ba.

Ratliffe yana yunƙurin farfaɗo da tagomashin Man United ne, inda ya ce burinsa shi ne kawar da Manchester City da Liverpool daga jagorancin gasar Firimiya.

A kwanakin baya ne Ratcliffe, attajirin ƙasar Ingila ya karɓi ragamar mallakar ƙungiyar bayan ya saka Fam biliyan £1 (Dala biliyan $1.2) ya sayi kashi 25% na hannun jarinta.

Yayin da kocin ƙungiyar Erik Ten Hag yake shekara ta biyu a matsayin manajan Man United, ana sa ran za su saka maƙudan kuɗi don sayan ‘yan wasa masu tsada a ƙarshen kakar bana.

KU KUMA KARANTA: Ba za a manta da Pele ba, in ji hukumar kwallon kafa ta FIFA

Rabon da Man United ta ci kofin Firimiya tun 2013, kuma a kakar bana ma suna mataki na shida ne a teburin na Firimiya, duk da dai sun kai matakin kusa da na ƙarshe a gasar FA, bayan doke Liverpool ranar Lahadi.

Yayin da Ratcliffe, wanda yake da shekaru 71 a duniya, ya fito a shirin ‘Cycling Club podcast da Geraint Thomas ke gabatarwa, an tambaye shi ko zai nemi sayan ɗan wasan tsakiya na Ingila Bellingham daga Real Madrid.

Ratcliffe ya ce, “Bellingham babban ɗan wasa ne, amma ba ya gabanmu. Mafitar da muke nema ba ta kashe maƙudan kuɗi kan sayo manyan ‘yan wasa ba ce”.

“An gwada haka a baya, idan ka duba shekaru 10 da suka wuce. An kashe tarin kuɗaɗe kan wasu tsirarun ‘yan wasa.

“Abu na farko da ya kamata mu yi shi ne mu nemo ‘yan wasan da suka dace a wajen da ya dace don gudanar da ƙungiyar. Kuma za mu tabbatar da mun ɗauko su, wannan shi ya fi dacewa da abin da ke faruwa a duniyar ƙwallo ta yau.”

A cikin shirin, an tambayi Ratcliffe idan zai zaɓi tsakanin sayo Kylian Mbappe na Faransa ga Man United, ko ɗan tseren keke Tadej Pogacar ga kulob ɗinsa na tsere na INEOS.

Ya ce, “Gara a ce na sayo wanda a nan-gaba zai riƙa ya zama kamar Mbappe, maimakon na zuba maƙudan kuɗi wajen sayen Mbappe na yanzu”.

Rahotanni sun nuna cewa Mbappe ya amince ya koma ƙungiyar Real Madrid daga Paris Saint-Germain a ƙarshen kakar bana.

Kuma ko da Mbappe yana kasuwa a yanzu, shahararren ɗan wasan ba zai iya cika buƙatun Ratcliffe ba.

Ratcliffe ya ƙara da cewa, “Sayan Mbappe ba wani abin birgewa ba ne. Kowa zai iya gane haka. Babban ƙalubalen shi ne nemo wanda zai iya zama tamkar Mbappe ko Bellingham ko Roy Keane a nan-gaba”.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Wasanni

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Published

on

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Ɗan wasan gaba na Inter Miami Lionel Messi ya jagoranci ƙasarsa Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America inda ta doke Canada da ci 2-0.

Messi mai shekaru 37 ya zura ƙwallo a minti shida da komawa daga hutun rabin lokaci.

Ɗan wasan Manchester City Julian Alvarez ne ya baiwa ƙasar wadda ke rike da kofin duniya damar samun wannan nasara bayan ƙwallon kusa da Rodrigo de Paul na Atletico Madrid ya buga.

Wannan dai shi ne karo na shida a karawa takwas da Argentina wacce ta lashe kofin Copa America sau 15 ta kai matakin wasan ƙarshe.

Wasan ƙarshen da Argentina za ta kara da Uruguay ko Colombia, zai kasance wasa na ƙarshe da Angel di Maria zai buga wa ƙasar kafin ya yi ritaya daga buga wasa sannan kuma akwai shakku kan makomar Messi.

”Za mu ji daɗin yanayin da muke ciki a matsayinmu na ƙasa kuma ƙungiya. Ba abu ba ne mai sauƙi kasancewarmu a matakin wasan ƙarshe domin sake fafatawa don zama zakara,” kamar yadda Messi ya shaida wa kafar TYC Sports.

Manajan Argentina Lionel Scaloni ya ce zai yi aiki don shawo kan Di Maria da Messi su ci gaba da buga wasannin ƙasa da ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Farin cikina ya dawo bayan komawa Inter Miami – Messi

“Yanayin Leo (Messi), yana kama da Angel,” in ji Scaloni.

”Dole ne mu bar shi ya yi abin da yake so, don ba za mu taɓa zama waɗanda za su rufe masa ƙofa ba, zai iya zama tare da tawagarmu har tsawon lokacin da yake so. kuma idan yana so ya yi ritaya kuma ya dawo ya kasancewa tare da mu, za mu yi farin cikin hakan.”

Jacob Shaffelburg, ɗan wasan ƙungiyar MLS Nashville ne ya ɓarar da mafi kyawun damar da Canada ta samu a farkon wasanta da Argentina.

Kasar Canada wacce ke matsayi na 48 a duniya, ta yi waje da ƙwallon da Alvarez ya zura a ragarta kana ya bai wa Argentina damar samun gurbi na gaba a wasan.

Duk da shan kayen Canada, tawagar ta yi rawar gani fiye da yadda ake zato a fafatawar da suka yi a gasar Copa America.

A ranar Lahadi ne tawagar Jesse Marsch wacce za ta ɗauki nauyin gasar cin kofin duniya ta 2026 tare da Mexico da Amurka, za su kara da wadanda suka sha kashi daga sauran wasan kusa da na ƙarshe a wasan neman matsayi na uku.

Continue Reading

Nishadi

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Published

on

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Jarumar TikTok, Sayyada Sadiya Haruna ta sake amarcewa a ranar Juma’a watanni kaɗan da mutuwar aurenta da jarumin TikTok Al Ameen G-Fresh.

A wani kati da ta wallafa a shafinta na Instagram, Sadiya ta bayyana sunan angon nata a matsayin Hon. Babagana Audu Grema.

An daura auren ne da misalin ƙarfe ɗaya bayan sallar Juma’a kamar yadda katin ya nuna a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin tarayya ta bai wa Rahama Sadau muƙami

Auren na zuwa mako guda bayan da jarumar ta TikTok ta bayyana a shirin tattaunawa na jarumar Kannywood Hadiza Gabon “Gabon Talk Show” inda Sadiya ta caccaki G-Fresh tare da bayyana matsalolin da suka kai ga mutuwar aurenta da shi.

Auren har ila yau na zuwa ne kwana guda bayan da shirin na Gabon ya watsa tattaunawar mayar da martani da G-Fresh inda shi ma ya yi ta sukar tsohuwar matar tasa – mafi aksarin lokuta a kaikaice.

Continue Reading

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like