Connect with us

Labari

Yadda Na Ji Da Aka Kashe ‘Yata Mai Ciki A Gidanta Da Ke Jigawa

Published

on

Daga; Rabo Haladu.

Mutane na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan rahoton mutuwar Ummi Garba, wata matar aure mai ciki da aka kashe a gidanta da ke ƙaramar hukumar Haɗeja a jihar Jigawa.

Masu amfani da kafafen sa da zumunta sun nuna kaɗuwa da takaicin wannan kisa da aka yi wa matar auren.

Mahaifinta da ake kira Malam Garba Umar ya shaida cewa wasu mutane ne suka shiga gidanta suka kashe ta.

A tattaunawar tasa da manema labarai, mahaifin Ummi ya ce ganin da ya mata na ƙarshe shi ne a ranar Lahadi lokacin da ta je bikin ƙanwarta gida.

Ummi ta zo gida a ranar Lahadi kuma tare muka wuni saboda ana bikin ƴar uwarta, kafin daga bisani mijinta ya zo ya ɗauke ta suka tafi, shi ne ganin da ya yi wa ƴar tasa na ƙarshe.”

“Ɗan uwana ne ya kira ni a waya ranar Laraba ya shaida mini cewa wasu mutane sun kashe Ummi, nan da nan na tafi gidanta, abin da idona ya gani na takaici ne kuma ba zan taɓa mantawa da hakan ba.”

Malam Garba ya ce a kan idonsa aka fitar da gawar Ummi a gidan da take zaune da mijin da ta aura wata 19 da suka gabata.

Ya tabbatar da cewa ‘yar tasa na ɗauke da ciki kamar yadda ma’abota shafukan sa da zumunta ke ta faɗa a shafukansu.

“Eh tana da juna biyu kuma tana zuwa awo, cikin shi ne na biyu bayan na farkon da ta samu wanda aka yi barin shi bayan wani lokaci.”

Ya ce ƴar tasa mai shekara 26 tana da biyayya kuma ba zai taba mantawa da ita ba.

A ƙarshe ya yi fatan cewa hukumomi za su yi abin da ya dace wajen gano wadanda suka yi wa ‘yar tasa kisan gilla.

A gefe daya, ‘yan sanda sun tabbatar da kisan matar, tare da cewa mijinta Mu’azu Babangida na asibiti yana karɓar magani.

A cewar kakakin ‘yan sandan Jihar Jigawa, DPS Lawal Adam, sun samu rahoton faruwar lamarin ne da misalin karfe 6:15 kan abin da ya faru, kuma da zuwan su suka tarar da Ummi cikin jini an kuma yanka wuyanta.

Ya ce “wani abu mai kaifi suka yi amfani da shi suka yanka wuyanta, lokacin da jami’anmu suka je wurin ta riga ta rasu.”

“Mijinta ya dawo daga aiki ya tarar da ita jina-jina a kwance, a yanzu da muke magana yana asibiti yana karɓar magani.”

Mutanen Hadeja dai sun ta nuna bacin ransu a Facebook kan wannan kisa da aka yi wa Ummi, kuma suna kira ga hukumomi su dauki matakin da ya dace cikin gaggawa.

Yusuf Muhammad Nadabo wanda ya wallafa hoton marigayoyar ya ce yana da mahimmaci hukumomi su mayar da hankali kan bankado wadanda suka yi aikin, ko dan zuciyar mutanen garin ta huce.

Hakazalika, a watan Fabrairun 2022, wasu mutane sun shiga gidan wata mata Rukayya Mustapha a Jihar Kano da ke arewacin Najeriya suka kashe ta.

Matar da ke zaune a unguwar Danbare ta mutu ne sakamakon dukan da aka yi mata in ji ‘yan sanda kuma an yi wa yayanta duka suma.

A watan Afrilun 2022, wani mutum da ake zargi shi ma ya kashe matarsa da ake kira Mercy Samuel a Jos a arewacin kasar, shi ma ya ja hankali.

.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like