Connect with us

Noma

Ya Kamata Ace Mun Yi Tsari Mai Kyau Da Zai Taimaki Kasa A Fannin Noma – Hon Munnir Babba

Published

on

Daga; Bashir Bello, Majalisa Abuja.

A YAYINDA kowani fanni ke daukar tsari na fasali mai nagarta a fadin Tarayyar Najeriya wanda hakan ke da nasaba da kawo cigaban harkoki, Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar karamar hukumar Kunbotso, Honarabul Munnir Babba Dan Agundi, kuma shugaban kwamitin kula da cibiyoyin da jami’o’in da kwalejin makarantu na Noma, ya bayyana cewa wajibi ne ayi tsari na musamman wanda zai taimaka wa fannin Noma a kasar.

Dan Majalisar Honarabul Munnir, wanda ya bayyana hakan a yayin zantawa da manema labarai, ya bayyana cewa Dokar da aka gyara a ma’aikatar mai kula da aikin binciken Noma da makarantun na Tarayya, ya biyo bayan yadda wadannan cibiyoyin ko ma’aikatun suke gudanar da harkokinsu tamkar yadda wasu kasashe kamar Indiya da Burazil suka bunkasa.

Ya kara da cewa a bisa Dokar da aka tsara wacce take ta hukumar bincike ta harkar Noma (ARCN) kuma ake dubawa don yin gyara ta yadda zai zama cewa duk wasu kwalejin makarantun Noma suna karkashin wata hukuma, wanda hakan zai sa a samu damar gudanar duk wasu harkoki ta yadda ya dace ba tare da an samu wata matsala ba domin wannan Dokar ta ARCN, za ta kawo gyare-gyaren da ake bukata.

Acewarsa, wasu daga cikin wadannan makarantun na da cibiyoyin bincike, hadi da wasu mambobin da suke tafiyar da harkokin bincikin amma a kan samu matsaloli wajen gudanar da harkokin sakamakon wasu yan siyasa ke yin katsalandan a cikin al’amuran, wanda harkar bincike irin wannan tana da bukatar mutane wadanda suke da kwarewa da dabaru da za suyi a fannin.

Ya ce “saboda irin wannan gyare-gyaren ne yasa muka ga cewa ya kamata ayi hakan domin sauran kasashen da muka je muka koyo aikin tare dasu duk suna ci gaba kuma duk sun fi mu bunkasa a harkar Noma bayan duk mun fara tare dasu ne, toh amma yanzu alhamdullah domin ta hanyar yin gyare-gyaren muna saran za a samu nasara wannan karon.”

“Kuskuren da aka samu wanda yake da bukatar gyara a yanzu dukda yake an sa hannu a takardar Dokar ita ce an turawa shugaban kasa takardar da suna cewa za a Kafa Makarantar a karkashin ma’aikatar Ilimi amadadin ma’aikatar Noma, toh kuma an gyara har shugaban Kasar yasa hannu domin tabbatar da an Kafa Makarantar ta zauna da gindin ta.”

“Toh wannan magana ce ta gyara kawai don haka ba wata matsala bace domin ina ganin abu ne na Ilimi kuma ana da bukatar mutane su samu ilimin domin cigaban kasa saboda sai da Ilimi zaiyu tunda idan ba Ilimi, babu ta yadda za ayi aci gajiyar tafiyar illa kawai muna bata lokacinmu ne.”

Shugaban Kwamitin ya ci gaba da cewa a Dokar da aka turo wacce zata sama wa cibiyoyin binciken hanyar samun Kudi kamar na TETFUND, wani abu ne wanda yake tsari mai Kyau domin kara inganta sashen harkar Noman domin tabbatar da wani tsari wacce zata rika tallafawa da kudaden da za a rika yin bincike saboda a yanzu basu da wani tsari wanda zaizo sai dai daga asusun Gwamnatin Tarayyar.

Da yake tsokaci kan batun gurbataccen man fetur wanda Majalisar ta bada matsayin ta a kai, Honarabul Munnir ya yaba da irin Matakan da majalisar ta dauka na ganin cewa an kawo Karshen samun matsaloli irin wannan ya Allah koda bisa kuskure, ko sakaci ko son rai ne ya haifar da wannan damuwar wacce ta ke addabar al’ummar Kasar a halin yanzu.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Bagudu ya halacci taron bunƙasa harkar noma a Abuja

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Sanata Abubakar Atiku Bagudu ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren tattalin arziƙi na ƙasa a ranar Talata 16/04/2024, Ya halarci wani shiri na musamman a babban birnin tarayya Abuja domin bunƙasa sha’anin harkokin ayukkan gona a faɗin Najeriya.

Shirin wanda yake ƙarƙashin gwamnatin ƙasar Jamus (Germany ) da kuma ƙungiyar GIZ zai bayar da gagarumar gudumuwa wajen bunƙasa sha’anin ayukkan gona a Najeriya.

Bagudu ya bayyana alfanun da ke akwai ta haɗaka da ƙungiyoyi ire-irensu GIZ ta hanyar musayar ilmi da amfani da zamani wajen cimma manufa, Bagudu ya ƙarfafawa mutanen da suka halarci shirin da su rinƙa shirya taron ƙara wa juna sani domin cimma kyakkyawar manufar ciyar da ƙasa gaba.

KU KUMA KARANTA: Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Bagudu ya ƙara fayyace cewar haɗaka na da matuƙar muhimmanci domin ta hakan ne za’a samu ci gaba a fannin tattalin arziƙi da ci gaba a Najeriya.

Continue Reading

Labarai

Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Published

on

Wasu manoman tumatur a ƙaramar hukumar Bagwai ta jihar Kano, sun koka kan yadda tsutsa ke lalata musu amfanin gona.

Manoman sun ce sun yi asarar amfanin gona da ta kai kusan Naira miliyan 500. Sun kuma ce tsutsar ta shafi kusan hekta 1000 na gonakinsu.

Wani manomin tumatir, Bello Idris ya ce suna cikin wahalhalu kan yadda tsutsar ta addabe su.

”Za mu nome tumatir mu sayi taki 50,000, mu kuma sayi maganin feshi 10,000 da man fetur amma duk a banza,” in ji shi.

Ya yi ƙira ga gwamnati da ta kawo musu ɗauki da kuma gano inda matsalar take.

KU KUMA KARANTA: Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Haka-zalika, shi ma Sama’ila Bello mazaunin karamar hukumar Dawakin Tofa, ya ce tsutsar na lalata musu amfanin gona cikin lokaci kankani.

“Muna so gwamnati ta taimaka mana a duba a ɓangaren iri ne ko maganin feshi ne ba a sayar da mai kyau,” in ji Bello.

Continue Reading

Labarai

Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Published

on

Gwamnatin Kebbi ta ɓullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin sauƙaƙa musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farfaɗo da aikin noma domin jihar ta cigaba da riƙe kambunta a ɓangaren noman shinkafa a Najeriya.

Saboda haka ne ta gina ƙaramin wurin noma na zamani a ƙananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, ƙari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.

KU KUMA KARANTA: An ceto manoma 16 daga hannun masu garkuwa da mutane a Neja

Ya ƙara da cewa gwamnatin jiha ta biya kasonta na naira miliyan 350 a cikin shirin RAAMP, wanda zai samar da hanyoyin mota masu tsawon kilo mita 240 domin manoma su samu saukin sufuri, gwamnati ta sanya miliyan 350 a shirin.

Shehu Mu’azu ya sanar da hakan a taron manema labarai na sati-sati da ma’aikatar yada labarai ta shirya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like