Connect with us

Labari

Wasu Mahara Sun Hallaka Sama Da Mutum 100 A Kanam Ta Filato

Published

on

Daga; Isah Ahmed, Jos.

WASU gungun mahara da ba a gane ko su waye ba, kan babura sama da guda 70, dauke da bindigogi sun kai hari, a wasu kauyuka a Karamar Hukumar Kanam da ke Jihar Filato, a safiyar ranar Lahadi a inda suka kashe sama da mutum 100 da kona gidaje sama da 100 da sace shanu masu tarin yawa.

Wasu ganau sun shedawa wakilinmu cewa, maharan sun kai harin ne a kauyukan Kukawa da Gyanbahu da Dungur da ke Karamar Hukumar Kanam da misalin karfe 11 na safiyar ranar Lahadi a inda suka kashe mutane da dama tare kona gidaje sama da 100 da sace shanu da dama.

An yi jana’izar sama da mutum 100, da aka gano gawarwakinsu a wadannan kauyuka, a ranar Litinin, kwana daya bayan kawo harin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Filato, ASP Ubar Gabriel ya bayyana cewa tuni rundunar su, ta tura jami’anta zuwa yanki amma bai fadi yawan adadin mutane da dukiyoyin da aka rasa ba.

To amma Shugaban Karamar Hukumar ta Kanam, Alhaji Dayyabu Yusuf Garga ya tabbatarwa da ‘yan jarida cewa, a kalla an kashe sama da mutum 100 a wannnan hari da aka kai.

“Ni da kaina tare da sauran jama’a mun ziyarci kauyukan da aka kai wannan hari. Kuma mun yi jana’izar sama da mutum 100, da aka kashe a wannan hari. Amma tuni an tura jami’an tsaro zuwa yankin don ganin an dawo da doka da oda”.

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong ya baiwa jami’an tsaro umarnin, su kamo maharan da suka kawo harin. Don ganin an hukumtasu kan wannan mummunan aika aika da suka aikata. Gwamnan ya bada wannan umarnin ne, a cikin wata sanarwa da Daraktan watsa labaran gwamnan, Dokta Makut Simon ya fitar.

Gwamnan ya yi nuna takaici tare da Allah wadai da wadannan hare hare da aka kai. Don haka ya bada tabbacin kamo wadannan mahara domin su fuskanci hukumci.

Jihar Filato dai, ta sha fama da rikice-rikice da ke da nasaba da kabilanci da addini, amma a baya-bayan nan ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa, sun ta’azzara matsalar.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like