Ilimi
Takaddamar Soke Mukamin Farfesan Pantami, Su Christ Piwuna Za A Ji Kunya
A ranar Litinin ne Ƙungiyar malaman jami’o’i a Najeriya ta ASUU ta yi watsi da matsayin Farfesa da aka bai wa ministan harkokin sadarwa da tattalin arziƙin zamani na kasar Dakta Isa Ali Pantami.
Jami’ar Tarayya ta Fasaha dake Owerri a jihar Imo ce ta ba shi matsayin na Farfesa, amma kungiyar malaman ta ce matakin haramtacce ne.
Ta kara da cewa za ta hukunta duk yayanta dake da hannu wajen bai wa Pantami matsayin.
Wannan matsaya da kungiyar ta yi, ya biyo karshen taron shugabanninta da aka gudanar a ranar Litinin, inda kungiyar ta bukaci Pantami da ya yi murabus daga matsayin minista sannan a gurfanar da shi saboda yin aiki biyu a ƙarƙashin gwamnati guda bisa saba ka’idojin da suka kamata a bi kafin akai ga bai wa Ministan matsayin Farfesa, kamar yadda mataimakin shugaban kungiyar ASUU ta kasa Chirst Piwuna ya fada.
A watan Nuwamban 2021 da ya gabata ne, jami’ar Tarayya ta Fasaha da ke Owerri ta ɗaga darajar Pantami zuwa Farfesa a ɓangaren tsaron intanet inda ta ce ya cika dukkan matakan da malaman jami’a ke bi kafin su samu matsayin mafi kololuwa a jami’a.
Kokarin jin ta bakin Pantami ya ci tura sai dai Ahmed Muhammad Pantami da ke zama dan’uwa ga ministan ya yi mana tsokaci.
“Wannan abin fa ba wai a shago ake sayensa ba, wannan mukami ba shi kadai aka ba, sun kai mutum hudu. Idan akwai abin da ya fi mukamin Farfesa ma ya kamata a ba shi.” In Muhammad Pantami.
Ko me tsarin doka ya ce game da irin wannan batu Barrister Umar Mainasara Kogo masani ne kan sha’anin sharia da kundin tsarin kasa.
“Babu wani wuri (a kundin tsarin mulkin Najeriya) da aka hana Farfesa Isa Ali Pantami zama Farfesa, sai dai kuma abin da yake tafe shi ne, idan har akwai wani kamar hurumi da su ASUU suke dauka na cewa shi bai cancanta ba, korafi ya kamata su rubuta zuwa hukumar jami’ar din da ta ba shi.” In Ji Barrister Mainasara Kogo.
Wannan ba shi ne karon farko da kungiyar ASUU ke fitowa ta kalaubalanci irin wannan batu ba.
Idan za’a iya tunawa ko a shekarar 2015 sai da kungiyar ASUU ta kalubalenci tsarin kara mukamai na wasu malamai daga jami’ar ayyukan noma ta Macheal Okpara Umudike dake jihar Abia lamarin da ya kai ga soke mukaman mutane da dama.
Ilimi
Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta
![Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240726-WA0008.jpg)
Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta
Daga Idris Umar, Zariya
Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.
Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.
Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.
KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal
Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.
A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.
Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.
Ilimi
Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal
![Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa - Dauda Lawal](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/05/IMG-20240528-WA0011.jpg)
Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal
Daga Idris UMAR, Zariya
Gwamna Dauda Lawal ya halarci taron yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu na Jami’ar tarayya, wanda ya gudana a filin taro na Jami’ar da ke Gusau a cikin satin da ya gabata
Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya shelanta bayar da gurbin karatu ga duk wanda ya zo na ɗaya a Jami’ar.
Cikin jawabinsa a wurin taron, Gwamnan ya yaba wa shugabannin Jami’ar game da yadda suka iya ririta ɗan abin da suke da shi, duk da ɗimbin ƙalubalen da suke fuskanta.
Ya ce, “Ina matuƙar farin cikin kasancewa da ku yau a wannan bikin yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu a wannan jajirtacciyar Jami’a, Jami’ar gwamnatin tarayya ta Gusau.
Ina taya jami’ar nan murnar samun wannan nasara, duk kuwa da matsalolin da suke fuskanta tun lokacin da aka kafa ta. Ina kuma yaba wa iyaye da ɗalibai bisa sadaukarwar da suka nuna har zuwa wannan matsayi.
Muna sa ran samun makoma mai kyau kuma mai albarka duk da tarin ƙalubalen da muke fuskanta a matsayinmu na jiha kuma al’umma.
Muna yin addu’a kuma muna aiki ba dare ba rana don samar da makoma mai kyau. Duk waɗannan matsaloli za su wuce da izinin Allah Maɗaukakin Sarki.”
Gwamnan ya yi ƙarin haske kan ƙoƙarin gwamnatinsa na gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara bayan kafa dokar ta-ɓaci a bara.
“A matsayinmu na gwamnati, mun ƙuduri aniyar ilimantar da duk ’ya’yan Zamfara. Ilimi shi ne ginshiƙin da ke haskaka ruyuwar ɗan adam.
“Mun ware maƙudan kuɗaɗe ga ɓangaren ilimi a cikin kasafin kuɗinmu na 2024 kuma muna fatan za mu kai ga babban matsayi a 2025, 2026, da 2027. Muna fatan cimma kashi 25 zuwa 30 na haɓaka tsarin ilimi.
Tare da samar da ingantaccen tsari a fannin da sarrafa albarkatun da ya ƙunsa, muna da ƙwarin gwiwar cewa za mu farfaɗo da ababen more rayuwa, ɗaukar ƙwararrun malamai, horarwa da sake horar da waɗanda ake da su.
“Za kuma mu ƙara yawan masu karatu a makarantun firamare da na gaba da firamare ta hanyar wayar da kan jama’a da samar da ingantattun wuraren koyo da koyarwa. Ilimi kyauta ne, kuma muna fatan ya zama wajibi ga kowa.
“Mun kuma yi wa manyan makarantunmu da ke jihar kason kuɗi mai yawa don fara aikin gyara su zuwa matakai masu inganci.
KU KUMA KARANTA:Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga
A karon farko Jami’ar Jihar Zamfara na shirye-shiryen amincewa da shirin Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa.
Mun umurci ’yan kwangilar da gwamnatin da ta shuɗe ta tilastawa barin wuraren aiki da su koma bakin aiki, kuma muna fatan nan da watanni masu zuwa, rukunin dindindin na jami’ar zai fara aiki. A lokaci guda, NUC za ta amince ga duk kwasa-kwasai.
“Mun karɓi mulki a jihar da gwamnati ta ƙi biyan kuɗaɗen jarrabawar WEAC da NECO har na biliyoyin Naira fiye da shekaru uku.
Dole muka yi shiri na musamman da hukumomin, kuma tun daga lokacin an fara biyan kuɗi a kan kari kuma za a kammala su a kan lokaci.
“A cikin ƙarancin albarkatunmu, za mu ci gaba da bayar da taimako ga jami’a. Burinmu shi ne mu ƙara haɓaka ilimi a jiharmu ta yadda za a samu damarmaki ga ɗaukacin matasanmu da za a horar da su don kai ga ƙololuwar da ilimi ke samarwa.”
Ilimi
Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/05/220px-Neco_official_banner.jpg)
Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO
Jami’o’in ƙasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO.
Shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa (NECO), Farfesa Ibrahim Wushishi, ya ce Jami’ar Lead da Jami’ar Birmingham City da ke kasar Birtaniya sun tuntubi hukumar kan jarabawar da take shiryawa.
Ya ce jami’o’in sun fara tunanin bai wa daliban Najeriya gurbin karatu da sakamakon jarabawarsu ta NECO.
KU KUMA KARANTA: JAMB zata duba yiwuwar amfani da wayoyin hanu a jarabawar UTME
A fahimtarsa, hakan na nuni da amincewa da ingancin sakamakon jarabawar NECO ne a idanun manyan jami’o’in ciki da wajen Najeriya.
Farfesa Wushishi ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa da ’yan jarida a Abuja ranar Laraba.
Ya ce NECO ta cika sharudan Jami’ar Birmingham City, kuma a halin yanzu suna aiki tukuru kan ganin sun sami cika sharudan jami’ar Lead.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai10 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Ibrahim Inuwa
February 16, 2022 at 11:19 pm
Hmmmmm