Connect with us

Noma

Rikicin Manoma Da Makiyaya: Kungiyar AFAN Da Miyetti Allah Zasu Samar Da Zaman Lafiya

Published

on

JABIRU A HASSAN, Daga Dutse.

KUNGIYOYIN manoma da makiyaya na Jihar Jigawa za su yi aiki tare domin magance yawaitar rikice-rikice da ake yi tsakanin manoma da makiyaya a Jihar, tare da jaddada hada hannu da gwamnatin Jihar ta Jigawa domin cimma nasarar wannan aiki.

Shugabannin kungiyar sune suka bayyana haka a tattaunawar su da wakilin mu a birnin Dutse, inda kuma suka nunar da cewa abubuwan da suka faru a makon da ya gabata a Jihar bai yiwa kowane bangare dadi ba.

Alhaji Idris Yau Mai Unguwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa wato (AFAN), ya bayyana cewa ko shakka babu rikicin da ya faru a yankin Guri tsakanin manoma da makiyaya bai yiwa kungiyar ta AFAN dadi ba, don haka zasu kara hada karfi da makiyaya domin daukar matakai na kawar da aukuwar fadace-fadace tsakanin bangarorin biyu.

Haka kuma ya sanar da cewa zasu ci gaba da kokari wajen ganin an kawo karshen rikici tsakanin manoma da makiyaya a Jihar ta Jigawa ta yadda za a ci gaba da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali duba da yadda kowane bangare yake da muhimmanci ga zamantakewar dan Adam”.

Mai Unguwar, ya yi amfani da wannan dama wajen yin Kira ga daukacin manoman Jihar Jigawa da su ci gaba da kasancewa masu bin doka da kaunar zaman lafiya kamar yadda aka san su, tare da jinjinawa gwamnatin Jihar Jigawa bisa jagorancin gwamna Muhammad Badaru Abubakar saboda kokarin da gwamnatin sa keyi wajen inganta zaman lafiya a fadin Jihar.

A nasa bangaren, shugaban kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah Alhaji Adamu Idris Babura, Kira ya yi ga makiyaya da su kara hakuri da nuna juriya wajen ganin an sami maslaha a duk lokacin da wata matsala ta faru, sannan ya jaddada cewa suna daukar Muhimman matakai na warware duk wata rashin jituwa da makiyaya suke ciki tsakanin su da manoma.

Haka kuma shugabannin sun yi amfani da wannan dama wajen yin ta’aziyya ga iyalai na wadanda suka rasa rayukansu yayin rikicin, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka sami raunuka sanadiyyar wannan rigima ta makiyaya da manoma.

Idan dai za a iya tunawa, an sami rikici tsakanin manoma da makiyaya a yankin Guri inda aka kashe mutane 3 da jikkata wasu mutane 15 wanda ya zuwa yanzu kungiyoyin guda biyu suka himmatu wajen ganin an sami kwanciyar hankali da maslaha dangane da abubuwan da suka faru.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Bagudu ya halacci taron bunƙasa harkar noma a Abuja

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Sanata Abubakar Atiku Bagudu ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren tattalin arziƙi na ƙasa a ranar Talata 16/04/2024, Ya halarci wani shiri na musamman a babban birnin tarayya Abuja domin bunƙasa sha’anin harkokin ayukkan gona a faɗin Najeriya.

Shirin wanda yake ƙarƙashin gwamnatin ƙasar Jamus (Germany ) da kuma ƙungiyar GIZ zai bayar da gagarumar gudumuwa wajen bunƙasa sha’anin ayukkan gona a Najeriya.

Bagudu ya bayyana alfanun da ke akwai ta haɗaka da ƙungiyoyi ire-irensu GIZ ta hanyar musayar ilmi da amfani da zamani wajen cimma manufa, Bagudu ya ƙarfafawa mutanen da suka halarci shirin da su rinƙa shirya taron ƙara wa juna sani domin cimma kyakkyawar manufar ciyar da ƙasa gaba.

KU KUMA KARANTA: Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Bagudu ya ƙara fayyace cewar haɗaka na da matuƙar muhimmanci domin ta hakan ne za’a samu ci gaba a fannin tattalin arziƙi da ci gaba a Najeriya.

Continue Reading

Labarai

Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Published

on

Wasu manoman tumatur a ƙaramar hukumar Bagwai ta jihar Kano, sun koka kan yadda tsutsa ke lalata musu amfanin gona.

Manoman sun ce sun yi asarar amfanin gona da ta kai kusan Naira miliyan 500. Sun kuma ce tsutsar ta shafi kusan hekta 1000 na gonakinsu.

Wani manomin tumatir, Bello Idris ya ce suna cikin wahalhalu kan yadda tsutsar ta addabe su.

”Za mu nome tumatir mu sayi taki 50,000, mu kuma sayi maganin feshi 10,000 da man fetur amma duk a banza,” in ji shi.

Ya yi ƙira ga gwamnati da ta kawo musu ɗauki da kuma gano inda matsalar take.

KU KUMA KARANTA: Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Haka-zalika, shi ma Sama’ila Bello mazaunin karamar hukumar Dawakin Tofa, ya ce tsutsar na lalata musu amfanin gona cikin lokaci kankani.

“Muna so gwamnati ta taimaka mana a duba a ɓangaren iri ne ko maganin feshi ne ba a sayar da mai kyau,” in ji Bello.

Continue Reading

Labarai

Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Published

on

Gwamnatin Kebbi ta ɓullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin sauƙaƙa musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farfaɗo da aikin noma domin jihar ta cigaba da riƙe kambunta a ɓangaren noman shinkafa a Najeriya.

Saboda haka ne ta gina ƙaramin wurin noma na zamani a ƙananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, ƙari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.

KU KUMA KARANTA: An ceto manoma 16 daga hannun masu garkuwa da mutane a Neja

Ya ƙara da cewa gwamnatin jiha ta biya kasonta na naira miliyan 350 a cikin shirin RAAMP, wanda zai samar da hanyoyin mota masu tsawon kilo mita 240 domin manoma su samu saukin sufuri, gwamnati ta sanya miliyan 350 a shirin.

Shehu Mu’azu ya sanar da hakan a taron manema labarai na sati-sati da ma’aikatar yada labarai ta shirya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like