Connect with us

Labari

Rikicin Filaye: ABU Ta Mayar Da Martani Ga KDSG, Ta Musanta Siyar Da Filin Ta

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A SAKAMAKON jin wata sanarwa wacce babban Daraktan Hukumar Tsare-Tsare da Cigaban Birane ta Jihar Kaduna (KASUPDA) Malam Isma’il Dikko ya yi bisa zargi cibiyar da sayar da filin ta, ya tayar da hankulan hukumar Jami’ar Ahmadu Bello inda ta musanta zancen sayar da filin mai kusan hekta 80 zuwa Kwalejin Aikin Gona da Dabbobi da ke Mando a cikin garin Kaduna ga daidaikun mutane.

A cikin wata sanarwa da aka sanya wa hannu Daraktan Hulda da Jama’a,
Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Malam Auwalu Umar ya ce zargin karya ne kuma ba shi da tushe, don Jami’ar Ahmadu Bello ba ta taba sayar da fili ga kowa ba, walau mutum ko kungiya, kuma ba za ta taba yin haka ba.

Ya ce “Kwalejin na da takardar shaidar mallakar (G.ITEM-No.1060) na daukacin kasar da aka kafa ta, baya ga Tsarin Binciken da ke nuna dukkan iyakokin Kwalejin”.

Auwalu Umar ya kara da bayyana cewa hukumomin Jami’ar sun yi wa kwalejin katanga ne shekaru da dama da suka gabata domin hana masu satar filayen su shiga kasarta. Sai dai a kwanakin baya KASUPDA da ake zargin tana aiki da umarnin gwamnatin jihar Kaduna, ta keta ka’ida ba bisa ka’ida ba, sannan ta rusa katangar da ke kan iyakokinta cikin rikon sakainar kashi, duk kuwa da umarnin kotu na ci gaba da dakatar da hukumar daga irin wannan haramcin.

“Hakika Darakta Janar na Hukumar Tsare-Tsare da Cigaban Birane ta Jihar Kaduna (KASUPDA), Isma’il Dikko, ya yi karya ta hanyar zargin hukumar da sayar da filayen ta ga daidaikun mutane.

Ya koka da yadda KASUPDA ta gaza yin gwaji mai sauki na gudanar da sahihin bincike don kaucewa kunyatar da gwamnatin jihar, watakila saboda tsananin son zuciya da kishinsa ta hanyar yin wannan zarge-zargen da ya yi”.

“Wannan wani mataki ne na ceto fuskar da Isma’il Dikko ya yi amfani da ita bayan da ya gane illar abin da ya aikata da laifin da ya aikata a Jami’ar”.

“Domin kaucewa shakku, ya kamata hukumar kula da tsare-tsare da raya birane ta jihar Kaduna ta san cewa, babu wani abin da zai sa ABU ta bari a karbe filayenta ba bisa ka’ida ba domin rabawa abokan tarayya da sauran marasa kishin kasa”.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like