Connect with us

Labari

FG, Na Kokarin Samar Da Hanyoyin Magance Matsalar Tsaro A Kasar – Boss Mustapha

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A KOKARIN da ake na samar da mafita mai dorewa kan kalubalen tsaro da ake fama da shi a shiyyar siyasar Arewa maso Yamma, Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na kara samar da hanyoyin magance matsalolin da suka shafi rashin tsaro a kasar nan ta kowane hali.

A ranar Alhamis yayin taron kwana biyu na masu ruwa da tsaki na taron karawa juna sani kan kalubalen tsaro da ake fuskanta a shiyyar yankin Arewa maso Yamma da ya gudana a Arewa House, Kaduna, tare da hadin gwiwar hukumar tuntubar tsaro da magance rikici, Boss Mustapha ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta damu da wadannan kalubale kuma tana aiki tukuru don rage su zuwa mafi ƙanƙanta.

Da yake wakilcin SGF a jawabin da ya gabatar, Mista David Attah ya kara da cewa, Najeriya na fama da matsalolin tsaro da dama a sassan kasar, inda ya kara da cewa kalubalen ya janyo asarar rayuka masu kima da kuma raba mutane da dama da kuma barnatar da dukiya ta biliyoyin Naira.

Ya ce “maganin rashin tsaro na daya daga cikin abubuwa uku (3) da gwamnati mai ci ta sa a gaba, ita ce wannan gwamnatin ta dauki matakai masu nisa don magance matsalar rashin tsaro a kasar nan, wasu daga cikin matakan sun hada da karin kasafin kasafi kamar yadda ya kamata da kuma kara yawan kayan aikin da ke rike da Sojoji da sauran hukumomin tsaro.”

“Hakazalika, an amince da daukar ‘yan sanda dubu goma (10,000) na tsawon shekaru uku (3) a jere yayin da aka kara duba albashinsu domin kara musu kwarin gwiwa, da kara kwazo don yin aiki tukuru, don haka abin farin ciki ne a lura da cewa yanayin magance matsalar tsaro ya samu ingantuwa a dukkan sassan kasar.”

“Sama da ‘yan tada kayar bayan dubu talatin da (30,000) da iyalansu ya zuwa yanzu sun mika wuya, bugu da kari kuma barazanar ‘yan awaren yankin Kudu maso Gabas da kuma wasu sassan yankunan siyasar yankin Kudu maso Kudu ya ragu matuka. yanzu hankalinmu ya kwanta kuma ba mu sake samun rahotannin hare-haren da masu zaman kansu ke kaiwa kullum.”

“Dakarun Operation SHARAN DAJI tare da jami’an rundunar ‘yan sandan Najeriya (NPF) da sauran jami’an leken asiri da jami’an tsaro da na soja sun ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan ta’addan, wanda a lokacin gwamnatin da dama ta dauki matakai masu nisa don magance matsalar rashin tsaro a kasar.”Inji Shi

A cewarsa, a karshen taron, za a karfafa wa mahalarta taron da su fadakar da sauran al’ummomin yankunansu muhimmancin kokarin hadin gwiwa wajen yaki da miyagun laifuka.

Shima da yake gabatar da nasa jawabin, gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa lokacin gudanar da taron ya dace, a matsayin wata shaida da ke nuna aniyar gwamnati na magance kalubalen tsaro da ake fama da shi, yayin da kuma zabar wurin da za a yi, ya nuna dabarun da Jihar Kaduna ke da shi ga kokarin hadin gwiwa na yaki da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

Gwamnan wanda kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Mista Samuel Aruwan ya wakilta, ya bayyana cewa a lokuta da dama matsalar rashin tsaro na da nasaba da ra’ayin nuna banbance-banbance, kuma idan aka yi la’akari da banbance-banbance Jihar Kaduna, wanda Jihar ta na da kimanin mutane miliyan 10, kana da kananan hukumomi 23 da kuma kabilu kusan 56.

Ya ce, “kamar yadda muka sani, babbar manufar gwamnati ita ce tsaro da jin dadin al’ummarta, matsalolin tsaro da ke fuskantar jihohin Arewa maso Yamma, musamman ‘yan bindiga da ta’addanci, wanda ya zama abin da bai dace ba kuma yake bukatar gwamnati, da kuma kungiyoyi daban-daban domin magance matsalar da ake fuskanta.”

“A zahirin gaskiya, an kafa wannan dandalin ne domin inganta kyakkyawar hulda a tsakanin kungiyoyin da suka dace a fadin yankin. An yi imanin cewa irin wannan huldar za ta amfanar da dukkan masu ruwa da tsaki da kuma sanya su wajen kawar da kalubalen da ake fuskanta a tsakanin al’umma ta yadda ya kamata da samar da matakan rukuni.”

“Idan aka yi rashin sa’a an siyasantar da al’amuran tsaro, masu aikata laifuka su kan jajirce tare da ba su garkuwa don zurfafa aikata laifuka da kuma yada ayyukansu na rashin jin dadi, shi yasa ako yaushe gwamnatin jihar Kaduna ta ke bayyana cewa duka ‘yan kasa gara su gwammace bin doka ta duk hanyar da ta dace koda za a jikkata.” A cewarsa

Daga karshe Malam Nasiru El-Rufa’i, ya mika godiyarsa ga ofishin SGF da sashen ayyuka na musamman, tare da yi wa kowa barka da zuwa Kaduna, tare da yi musu fatan alheri.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like