Connect with us

Labari

Al’ummar Garin Panbegua Sun Yabawa Gwamna El-Rufa’i Da FARMTRAC Bisa Aikin Hanya

Published

on

Daga Rabo Haladu

AL’UMMAR Ganin Panbegua da na garin Kauru duk a cikin kananan hukumomin Kubau da Kauru dake jihar Kaduna sun dade suna fuskantar matsalar rashin hanya, wanda yanzu gwamnatin Jihar Kaduna Ta bada kwangilar ginawa domin suma amfana da romon mulkin damokuradiyya.

Hanyar Pambegua zuwa Garin Kauru hanya ce wadda shekara da shekaru al’ummar yankin musamman manoma suke neman gwamnatin Jihar tayi musu amma hakan yaci tura, hasalima hanyar wacce manoman yankin suke fuskantar matsalar jigilar amfanin gona.

Al’ummar sunce bisa ganin yadda gwamnatin Jihar Kaduna da Kamfanin FARMTRAC suka himmatu wajen aiwatar da aiki mai inganci, hakan yasa suke jinjiwa Kamfanin da Gwamnatin Jihar Na cewa yanzu suma zasu dare wajen cin gajiyar ayyukan Gwamnatin El-Rufa’i na raya kasa da al’umma.

Honarabul Shehu Yunusa Pambegua, shi ne dan majalisar dokokin Jihar Kaduna mai wakiltar mazabar Kubau, wanda kuma mazaunin garin Pambegua ne, ya bayyana cewa aikin hanyar yazo dai dai lokacin da Al’ummar suke bukantarsa wanda idan aka kammala ta al’ummar yankin wadanda mafi yawansu manoma ne zasu samu saukin jigilar amfanin gona da kuma bunkasa harkokin kasuwanci baki daya.

“ Matsayina na dan asalin wannan karamar hukumar naji dadi sosai da naga Kamfani na gida yana aiwatar da aiki mai inganci da nagarta, wani abin mamaki da jin dadi mutanan Garin sun tabbatar min da cewa baya ga aikin da Kamfanin yake yi shi Kansa mai Kamfanin yakan yi musu alheri idan ya Kawo ziyara. Gaskiya mun godewa gwamnatin Jihar Kaduna da Kamfanin FARMTRAC a kan wannan aikin hanyar wanda zai amfani dubban mutane bama yan yankin kadai ba” inji Shi

Daniel Duniya shi ne mataimakin shugaban kungiyar ‘yan Jarida ta kasa NUJ reshen Jihar kaduna, ya bayyana cewa babu abin da zasu cewa gwamnatin Jihar Kaduna sai godiya saboda sama da shekaru goma suna neman a yi musu hanyar amma hakan ya faskara.

Duniya wanda ma’aikaci ne a gidan Rediyon Jihar Kaduna (KSMC) ya yaba kokarin dan kwangilar na fara aikin babu kama hannun yaro, inda ya yi fatan gwamnatin Jihar za ta ci gaba da shimfudo wa mutanan karkara ayyukan raya yankunan su.

Alhaji Hussaini Dan Allahji, direba ne, a garin Panbegua ya bayyana cewa duk wani direban Mota mai zirga-zirga daga Panbegua zuwa garin Kauru har ya wuce kasuwar magani yasan yadda hanyar ta lalace duk kuwa da cewa ita ce hanyar da manoma suke amfani da ita wajen kai kayan abinci gida da kasuwanni.

Akan hakan ya bayyana jin dadinsu da matakin da gwamnatin Jihar Kaduna ta dauka na gina hanyar.

“Ya zama dole mu jinjinawa Dan kwangilar dake aikin hanyar bisa aiwatar da aiki mai inganci wanda bisa alamun da muke gani aikin zamu dade muna amfana dashi. Idan ka duba yadda suka fara aikin, gaskiya babu abin da zamuce sai godiya”

Shima a zantawarsa da wakilinmu ta wayar tarho shugaban Kamfanin na FARMTRAC Injiniya Sadiq Abubakar, ya ce Kamfanin su ya himmatu wajen ganin ya fito da martabar sunan kamfanonin cikin gida ta hanyar aiwatar da aiki mai inganci da nagarta inda yace Kamfanin sa zai tabbatar da cewa ya yi aikin da al’ummar Jihar kaduna zasu amfana na tsawon lokaci.

Injiniya Saddiq, haka zalika, ya dauki alwashin cewa duk wani aiki da gwamnatin Jihar kaduna zata bashi zaiyi shi mai inganci da nagarta kamar yadda Kamfanin ya yi na raya Garin Kachia da Kafanchan wajen shinfuda musu titi mai nagarta da sauran wurare a fadin Jihar kaduna baki daya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like