Connect with us

Labari

Sanata Uba Sani Ya Bayar Da Kyautar Mota Ga Kungiyar NUJ Kaduna

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

DAN takardar Gwamnan Jihar Kaduna karkashin Jam’iyyar APC, Malam Uba Sani, kuma Sanata mai ci dake wakiltar Jihar Kaduna ta tsakiya a zauren majalisar dattawa a ranar Laraba ya bayar da kyautar mota ga kungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna..

Sanatan Uba Sani, daya samu wakilcin babban Jami’in mazabarsa na shiyya, Abubakar Rabi’u Abubakar, ya bayyana cewa an bayar da motar mai kirar salun ne domin inganta al’amuran da harkokin sufuri na cibiyar Kungiyar wajen tabbatar da isar da aikinsu na tattarawa da yada bayanai ga jama’a.

Ya ce makasudin samar da motar ga cibiyar Kungiyar NUJ Kaduna, ya samo asali ne daga doguwar alaka da yake da ‘yan jaridu.

“Wannan gudummawar ita ce hanyarmu ta bayar da tamu gudunmawar don taimakawa wajen yada labarai masu inganci da gaggawa daga Kungiyar, da kuma tsara al’amuran jama’a ta hanyar wayar da kan jama’a don sanin hakikanin abin da ke faruwa a harkokin mulki a Kaduna,” inji shi.

Sani ya kuma kara da cewa an bayar da tallafin ne domin zaburar da mata ganin cewa kungiyar Kaduna na da mace a matsayin shugabar farko da ke gudanar da harkokin cibiyar Kungiyar.

“Kamar yadda kuka sani, ni da gwamnan Jihar Kaduna, a kodayaushe muna son ganin mata suna rike da mukamai a cikin Gwamnati, suna gudanar da bincike kan al’amuran wurare masu mahimmanci a cikin al’umma.

“Muna matukar sha’awar kafofin watsa labaru, kuma hakan yana sanar da ra’ayinmu game da gudummawar, tare da yin duk damar da za ta halarci ayyukan watsa labarai lokacin da aka gayyace mu.

“Taimakon ya zo daidai da motoci 59 da muka bayar kwanaki biyu da suka gabata don yakin neman zabe, a gaskiya muna da sha’awar ci gaban ’yan jarida, kuma wannan ba shi ne karon farko da za mu bayar da gudunmawa ta wata hanya ko wata ba don samun nasarar su,” inji Sani.

Da take karbar makullin motar, da kuma takardar, shugabar kungiyar NUJ Kaduna, Hajiya Asma’u Halilu, ta godewa Sanatan bisa wannan karimcin.

Ta ce samun motar a matsayin abin hawa ga Kungiyar wata nasara ce kuma hakan zai yi tasiri wajen rage musu zirga-zirga.

“Mun zo ne a lokacin da Kungiyar ba ta da abin hawa kuma yau da yardar Allah Sanata Uba Sani ya ba mu daya,” inji Asma’u

Ta kuma yi addu’ar Allah ya taimaki Sanatan ya cim ma burinsa ya kuma ba shi zuciyar ci gaba da ciyar da al’ummar mazabar sa da ma mabukata baki daya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like