Connect with us

Siyasa

Najeriya Na Da Bukatar Tsayayyen, Jajirtaccen Mutum Kamar Ni – Bukola Saraki

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A BISA yunkurin da yake na ganin cewa ya samu shugabancin Kasar Najeriya, Tsohon Gwamnan Jihar Kwara kuma Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Dakta Abubakar Bukola Saraki, ya yi ikrarin cewa Kasar Najeriya na da bukatar tsayayyen mutumi kuma jajirtacce wanda zai iya kai ta ga tudun mun-tsira.

Dan takarar Shugabancin Kasar Najeriya, Sanata Bukola Saraki, ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da wakilan Jam’iyyar PDP a garin Kaduna, a ranar lahadi domin neman goyon bayansu a bisa kudirinsa na neman Jam’iyyar ta tsayar da shi a matsayin dan takarar ta.

Ya kara da cewa kamar yadda kowa ya sani, shi mutum ne wanda yake mai kishin al’umma kuma jajirtacce wanda ya saba nuna bajintarsa a fagen daga wajen ganin ya kare hakkin al’umma tare da kawo musu ci gaba ta kowani fanni don tabbatar da adalci a tsakaninsu.

Ya ce “shekarar 2023, lokaci ne da ba za ace an zabi kowani irin mutum ba a matsayin Shugaban kasa, kuma duk mun san cewa babu ta yadda za ayi a samu mulki ba tare da sa albarkarku yan Kaduna ba saboda mahimmanci ku, don haka nayi takakkiya na kawo kaina domin neman amincewa da goyon bayan ku ta yadda zan zama Shugaban Kasar Inshaa Allahu.”

“Wannan Kasar na cikin mummunar yanayi kuma babu wanda ya fi ku yan Kaduna sanin wannan yanayin domin a shekarun baya, ba dare ba rana mutane na iya zirga-zirga amma yanzu lamarin rashin tsaro ya lalata al’amura, saboda haka nake son ku bani damar da zan yi gyaran da zai canza al’amura ta yadda za a samu waraka wajen tafiyar da al’amura.”

“Wannan kasar nan na da bukatar wani jajirtaccen mutum wanda Kasar ce kawai a zuciyarsa kuma a shirye yake da ba da rayuwarsa wajen ganin ya yi halacci ga al’umma tare bunkasa dukkan al’amura da tattalin arzikin Kasar, kuma kunsan na kasance mutum ne wanda ya ke dauke da duka irin wadannan shiffar musamman a lokacin da nake Shugaban Majalisar Dattawa.

“Kuma a matsayina na likita, na yi muku alkawarin cewa muddun kuka zabe ni har na kai ga zama Shugaban kasa, zan tabbatar da duk wani dan kasa na zuwa asibiti kyauta, musamman iyayenmu mata domin wannan wani abu ne da na taba jaraba shi kuma yayu ayayin da nake Gwamna a Jihar Kwara, sannan na yi alkawarin kawar da duk wata matsalar tsaron da kuke fuskanta ana Kaduna.

“Ba zan taba gajiyewa ba har sai naga na tabbatar da na kawar da matsalar rashin tsaro da ta’addanci ta yadda kowa zai iya gudanar da harkokinsa ba tare wani shakku ko tsoro ba, yaranku su je Makaranta cikin kwanciyar hankali domin a yanzu talauci ya yiwa al’umma yawa, babu kwanciyar hankali don haka muke bukatar wannan canjin wanda ni zan kawo muku shi cikin yardar Allah.

Sanata Abubakar Bukola Saraki, ya godewa Ya’yan Jam’iyyar PDP ta Kaduna, bisa irin karamcin da suka nuna mishi tare da neman tabbacin goyon bayansu na ganin ya cimma nasarar wannan kudirin nasa na zama Shugaban Kasar Najeriya a zaben shekarar 2023 mai zuwa.

Da yake jawabi amadadin Dattawan Jam’iyyar PDP na Jihar Kaduna a wajen taron, tsohon Gwamnan Jihar, Dakta Muktar Ramalan Yero, ya yabawa dan takarar bisa ziyarar tare bayyana cewa, tabbas shi mutum ne mai natija da rike alkawari, kana jajirtacce wanda ya nuna kwazonsa a baya kuma zai iya yin duk wani abu na ganin cewa ya ciyar da kasar gaba.

Dallatun Zazzau, ya ci gaba da cewa, a irin sanin da ya yiwa Dan Takarar Kujerar Shugabancin kasar, a matsayin abokin aiki, Shugaban Gwamnoni da abokinsa, mutum ne wanda yake da kwarewa ta fanni daban-daban kuma yake Kokarin ganin ya aiwatar da al’amura yadda ya kamata, don haka suna fatan idan Allah Ya kai shi ga zama Shugaban Kasar, ya tabbatar da an kawar da matsalar rashin tsaro daya addabesu a Birnin Gwari don wannan ita ce babbar matsalar su.

A karshe, Ramalan Yero, ya tunatar da Dan takarar Sanata Abubakar Bukola Saraki da cewa ya sani Mulkin na Allah ne, amma suna goyon bayan shi dari bisa dari domin tabbatar da ya kai ga samun shugabancin Kasar a zaben shekarar 2023 mai zuwa cikin yarda da ikon Allah.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like