Connect with us

Siyasa

Muna Biyayya Ga Gwamna Ganduje Da Uwar-Gidansa – Inji Hajiya Alpha Dambatta

Published

on

JABIRU A HASSAN, Daga Kano.

WATA Jigo a jam’iyyar APC daga Karamar hukumar Dambatta wadda Kuma aka fi sani da “Maman Maja” watau Hajiya Alpha Abdul Usman Dambatta, ta ce suna nan tare da gwamna Dokta Abdullahi Umar Ganduje da kuma mai dakinsa a tafiya irin ta siyasa domin ci gaban Jihar Kano.

A cikin wani shiri da wata kafar labarai ta yi da ita, Hajiya Alpha Abdu Usman Dambatta wadda Kuma har ila yau ake Yi Mata kirAri da Uwar marayu, ta bayyana cewa a siyasar wannan zamani, gwamnatin Jihar Kano bisa jagorancin Gwamna Dokta Abdullahi Umar Ganduje ta yi kokari kwarai da gaske wajen tabbatar da cewa al’ummar Jihar Kano suna rabauta da ribar dimokuradiyya ba tare da nuna gajiyawa ba tun daga shekara ta 2015.

Sannan ta nunar da cewa al’ummar Jihar Kano sun yarda cewa gwamnatin Ganduje ta yi kokari sosai wajen bunkasa Jihar ta fannoni daban-daban duk da irin kalubalen da aka rika cin karo dasu kamar yadda tsarin dimokuradiyya ya gada tun da kasarnan ta koma kan tsarin mulkin siyasa a shekara ta 1999.

Haka kuma Maman Maja, Hajiya Alpha Dambatta ta bayyana mai dakin Gwamnan, Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje a matsayin uwa tagari wadda kuma take da kishin al’ummar Jihar Kano musamman mata da matasa da Kuma yara kananana da suke da matukar bukatar tallafi.

Ta yi amfani da wannan dama inda ta godewa Gwamna Dokta Abdullahi Umar Ganduje da Uwargidansa Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje saboda kokarin da suke yi wajen ganin suna kyautata zamantakewar al’ummar jihar Kano ta kowane fanni ba tare da nuna gajiyawa ba, wanda a cewar ta jihar kano ta zamo abar misali cikin Jihohin wannan kasa.

Dangane da abubuwan da suke faruwa na rikicin cikin gida a jam’iyyar APC a kano kuwa, Hajiya Alpha Dambatta ta ce wannan ado ne a dimokuradiyya, amma gwamna da dukkanin masu ruwa da tsaki suna kokarin kawo daidaito a tafiyar da siyasar jihar duba da yadda yanzu an dauki matakai na kara karfin jam’iyyar musamman wajen fitar da Yan takara a dukkanin matakai da za a fafata dasu a zaben 2023.

A karshe, Hajiya Alpha Abdu Usman Dambatta, uwar marayu, ta yi fatan ci gaba da samun dawamammen zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Kano da Kuma kasa baki daya ta yadda zabukan da za a gudanar zasu zamo masu albarka ga al’ummar kasa baki daya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like