Connect with us

Siyasa

PDP-NYA Ta Taya Ashiru Kudan Murnar Lashe Zaben Fidda Gwani, Ta Jinjinawa Jam’iyyar Ta PDP

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WATA kungiyar matasa ta Jam’iyyar PDP wato People’s Democratic Party National Youth Agenda, (PDP-NYA) reshen Jihar Kaduna, ta taya Rt. Hon. Isah Ashiru Kudan murna lashe Zaben fidda gwani a yayin da ya zama dan takarar gwamna da ke rike da tikitin jam’iyyar a jihar, ta kuma yabawa jam’iyyar bisa gudanar da zaben fidda gwani na gaskiya da lumana a jihar.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar (PDP-NYA) na Jihar, Kwamared Ahmad Ashir ya sanya wa hannu, ya bayyana jin dadinsa bisa nasarar da dan takarar ya yi tare wakilan jam’iyyar bisa kokarin ganin an samu dan takarar jam’iyyar da zai yi zarra a zaben duka gari mai zuwa na shekarar 2023.

Kwamared Ashir ya kara da cewa, zabin da ke gabansu a zaben fidda gwani na 2022 shi ne tsakanin shugabanni nagari da miyagu, kuma tsakanin wakilcin da ya dace na al’umma da kuma na bata suna. Tsakanin shugabannin da za su kasance tare da jama’a tun daga farko bayan sun ci zabe har zuwa karshen wa’adinsu da kuma Shugabannin da za su yi watsi da jama’a bayan sun cimma burinsu amma daga baya su fara tuntubar mutane idan lokacin wani zabe ya yi.

Ya ce, “zabe ne tsakanin shugabanni ne da suka wawure mana biliyoyin Naira na ayyukan mazabunmu da kuma shugabannin da ke da muradin sauya rayuwar Talakawa gobe.

“Na biyu, zabe ne tsakanin shugabanni da za su rika bin al’adar ba mu abinci su sayi kuri’unmu da kuma shugaban da ke da muradin tallafawa kan yadda za mu sayi kayan abincin kanmu a rayuwarmu, zabe ne tsakanin shugabannin da ba ruwansu game da mutanensu da ake kashewa da shugabannin da suka shirya don kare jama’a.

“Zabe ne tsakanin shugabannin da suke ganin siyasa wata dama ce ta yin hidima don amfanin kowa da kuma shugaban da yake kallon siyasa a matsayin kasuwanci ne suke wawure duk wasu kudaden da ake son ci gaba. To, sai yaushe za mu kasance cikin talauci da dukiyar mu?” Ya tambaya

“Wakilan Jam’iyya, shugabanni da masu ruwa da tsaki a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP reshen jihar Kaduna, kun zaba mana zabin mu mai girma Sarkin Bai Zazzau Honarabul Isah Ashiru Kudan wanda zai gyara rayuwar kowa a yau da gobe idan Allah ya kaimu a Jihar Kaduna.

“Kun sauke nauyin da ya rataya a wuyanku a jihar ku ta hanyar yanke wannan shawara mai kyau na zaben shugaban da ke shirye ya yiwa talakawa aiki, mutum mai tausayin dan Adam da kwarjinin shugabanci.

“Saboda haka, ina kira ga wadanda suka yi nasara kuma da wadanda suka fadi zaben fidda gwani tun daga majalisun Jihohi da na Wakilai da na Sanata da kuma na Gwamna da su dauki kansu a matsayin iyali daya mu hada kai domin samun nasarar hadin kan Jam’iyyarmu da kuma Jihar musamman domin tabbatar da cewa Jihar mu ta dawo daga fagen mulkin mallaka rashin shugabanci nagari” Inji Kwamared Ashir.

Ya kara da nanata cewa (PDP-NYA), Kungiya ce da ke aiki a kowane mataki na ci gaban jam’iyyar da kuma matasa baki daya ta hanyoyin dabarun ci gaban jama’a da wayar da kan jama’a kan muhimmancin zaben jam’iyyar kamar yadda suke da karfin jefa kuri’a.

A karshe Shugaban na Jiha, ya bayyana cewa za su ci gaba da bayar da goyon bayansu, tattaunawa da kuma zaburar da masu kada kuri’a ga daukacin ‘yan takarar jam’iyyar PDP tare da goyon bayan jam’iyyar PDP ta Kaduna da kuma fatan karbar madafun iko a 2023.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like