Connect with us

Noma

Muhalli: Wani Dan Najeriya Na Shuka Nau’in Bishiyoyi Sama Da Dubu 100.000 A Duk Shekara

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WANI hamshakin attajiri dake Jihar Kaduna a Kasar Najeriya, Al-amin Shehu, kuma ya ke da matakin karatun digiri, ya yi watsi da aikin farar fata, yayin da ya rungumi yin shuka da sayar da itatuwan domin dogaro da kansa, tare da tallafa wa gwamnati, kungiyoyin farar hula na Najeriya, kungiyoyi masu zaman kansu domin yaki da sauyin yanayi, bala’in ambaliya, kwararowar hamada, wanda aikin sare dazuka da lalata muhalli ke shafar rayuwar Bil-Adama da sauran kungiyoyin agaji.

A cewarsa a kowace shekara, sama da nau’ikan tsire-tsire daban-daban dubu dari yake shukawa tare da sayar wa dubban mutane da nufin dasa su a gida, tituna, da sabbin wurare domin ceton dan Adam daga dumamar yanayi da sauran kalubalen muhalli.

Al-amin, wanda bayan ya kammala karatunsa, ya rungumi sana’ar shuka iri da sayar da bishiyu domin ya kare kansa kuma ta wannan sana’a yake samun abin da yake samu na rayuwa kana a cikin kowane wata 6, yana samar da nau’ikan itatuwa dubu hamsin.

Ya kara da cewa ba ya son duk wani aikin gwamnati domin yana jin dadin abin da yake samu a kasuwanci, kuma hakan ya sanya ya ke kalubalantar wadanda suka kammala karatun digiri dinsu da zama masu kirkire-kirkire ta yadda zasu iya dogaro da kansu.

Bugu da kari, ya yi da kira ga gwamnati da ta samar da yanayin da zai sa wadanda suka kammala digiri su kasance masu dogaro da kai.

Hakazalika, wani masanin kimiyyar climatologist, darektan masu ba da rahoto kan yanayin yanayi na Afirka, Kwamared Nurudden Bello, ya buƙaci yan Najeriya da su dasa itatuwa da yawa a bana, domin yaki da kwararowar hamada, da rage dumamar yanayi.

Ya yi nuni da cewa dazuzzuka da dama a Arewacin Najeriya sun koma saharar hamada sakamakon rashin hankali da mutane suke yi na sare itatuwa.

Yayin da yake jaddada bukatar ‘yan Najeriya su rungumi dabi’ar dashen itatuwa a cikin al’ummarsu, ta yadda za a ceto muhalli daga bala’in ambaliyar ruwa, zaizayar kasa, da sauran kalubalen da suka shafi muhallin da ke cikin ruwa, ya nuna rashin jin dadinsa kan karuwar bukatar sana’ar sayar da itace da gawayi a kasar nan.

A karshe, ya yi kira ga gwamnati a dukkan matakai da su rungumi amfani da makamashin zamani da sauran hanyoyin amfani da murhun girki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Bagudu ya halacci taron bunƙasa harkar noma a Abuja

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Sanata Abubakar Atiku Bagudu ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren tattalin arziƙi na ƙasa a ranar Talata 16/04/2024, Ya halarci wani shiri na musamman a babban birnin tarayya Abuja domin bunƙasa sha’anin harkokin ayukkan gona a faɗin Najeriya.

Shirin wanda yake ƙarƙashin gwamnatin ƙasar Jamus (Germany ) da kuma ƙungiyar GIZ zai bayar da gagarumar gudumuwa wajen bunƙasa sha’anin ayukkan gona a Najeriya.

Bagudu ya bayyana alfanun da ke akwai ta haɗaka da ƙungiyoyi ire-irensu GIZ ta hanyar musayar ilmi da amfani da zamani wajen cimma manufa, Bagudu ya ƙarfafawa mutanen da suka halarci shirin da su rinƙa shirya taron ƙara wa juna sani domin cimma kyakkyawar manufar ciyar da ƙasa gaba.

KU KUMA KARANTA: Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Bagudu ya ƙara fayyace cewar haɗaka na da matuƙar muhimmanci domin ta hakan ne za’a samu ci gaba a fannin tattalin arziƙi da ci gaba a Najeriya.

Continue Reading

Labarai

Tsutsa ta janyo mana asarar naira miliyan 500 – Manoman tumatur a Kano

Published

on

Wasu manoman tumatur a ƙaramar hukumar Bagwai ta jihar Kano, sun koka kan yadda tsutsa ke lalata musu amfanin gona.

Manoman sun ce sun yi asarar amfanin gona da ta kai kusan Naira miliyan 500. Sun kuma ce tsutsar ta shafi kusan hekta 1000 na gonakinsu.

Wani manomin tumatir, Bello Idris ya ce suna cikin wahalhalu kan yadda tsutsar ta addabe su.

”Za mu nome tumatir mu sayi taki 50,000, mu kuma sayi maganin feshi 10,000 da man fetur amma duk a banza,” in ji shi.

Ya yi ƙira ga gwamnati da ta kawo musu ɗauki da kuma gano inda matsalar take.

KU KUMA KARANTA: Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Haka-zalika, shi ma Sama’ila Bello mazaunin karamar hukumar Dawakin Tofa, ya ce tsutsar na lalata musu amfanin gona cikin lokaci kankani.

“Muna so gwamnati ta taimaka mana a duba a ɓangaren iri ne ko maganin feshi ne ba a sayar da mai kyau,” in ji Bello.

Continue Reading

Labarai

Jihar Kebbi za ta raba man fetur kyauta ga manoma

Published

on

Gwamnatin Kebbi ta ɓullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin sauƙaƙa musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farfaɗo da aikin noma domin jihar ta cigaba da riƙe kambunta a ɓangaren noman shinkafa a Najeriya.

Saboda haka ne ta gina ƙaramin wurin noma na zamani a ƙananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, ƙari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.

KU KUMA KARANTA: An ceto manoma 16 daga hannun masu garkuwa da mutane a Neja

Ya ƙara da cewa gwamnatin jiha ta biya kasonta na naira miliyan 350 a cikin shirin RAAMP, wanda zai samar da hanyoyin mota masu tsawon kilo mita 240 domin manoma su samu saukin sufuri, gwamnati ta sanya miliyan 350 a shirin.

Shehu Mu’azu ya sanar da hakan a taron manema labarai na sati-sati da ma’aikatar yada labarai ta shirya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like