Connect with us

Siyasa

Matan Arewa Don Tinubu Sun Bukaci Masu Ruwa Da Tsaki Na APC Su Marawa Burin Bola Tinubu Baya

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

GABANIN zaben fidda gwanin Jam’iyyar (APC) mai zuwa, kungiyar Matan Arewa domin Tinubu wato (Arewa Women for Tinubu), ta yi kira da masu ruwa da tsaki a kasar nan da su marawa burin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu baya a yunkurinsa na kawo sauyi a kasar nan don samun kyakkyawar makoma.

Shugabar kungiyar Hajiya Sa’adatu Garba Dogon Bauchi ta bayyana haka ne a lokacin da take zantawa da manema labarai a ranar Laraba yayin wani taro da aka gudanar a garin Kaduna, inda ta bayyana cewa, Tinubu ya kasance dan takarar shugaban kasa daya tilo da ke da kasar a zuciyarsa.

Sa’adatu ta kuma bayyana Tinubu a matsayin mutum mai gaskiya, mai gina al’umma, inda ta ce yana da sha’awar tallafa wa sana’o’in mata da kuma son cika burinsu na siyasa.

Ta kara da cewa, makasudin gudanar da taron shi ne domin neman goyon baya ga Asiwaju Bola Ahmed Tinubu daga mahalarta taron kan burinsa na zama shugaban kasar Najeriya a shekarar 2023.

Hajiya Sa’adatu ta kuma roki wakilan Jam’iyyu na kasar da su fara yin la’akari da yanayin muradin kasar ta hanyar zaben mutane masu gaskiya da za su iya kawo ci gaba mai kyau a lokacin zaben fidda gwani na Jam’iyyar.

Bugu da kari, ta shawarce su da kada su fifita samun kudi a kan hakkokin da ake bukata game da ‘yan takarar da ke da tarihin da ake iya gani.

Ta ce, “game da batun masu zaben yan takara, zan iya ba da shawarar cewa kada su nemi kudi, su zabi wadanda suka dace, domin kudin nan za su kare, don haka su duba rayuwar ‘ya’yanmu da jikokinmu.”

Ta ci gaba da cewa, nasarar da dan takarar shugaban kasar ya samu a karkashin jam’iyyar APC na da yawa musamman kan yadda ya canza tare da bunkasa Jihar Legas a lokacin da yake gwamna.

A nasa jawabin, Sanata Sani Saleh ya ce taron an yi shi ne domin sanar da mahalarta taron bukatar yin kira ga wakilan jam’iyyar APC da su zabi Tinubu.

Ya kara da cewa, daga cikin duka yan takarar Shugabancin Kasar, babu wani dan takarar da yafi cancanta a yanzu da zai iya warware matsalolin da ake fuskanta a kasar fiye da Bola Tinubu wanda ya yi a shekarun baya dukda suna yar-tsama da Shugaban Kasar lokacin, kuma kowa ya shaida Jajirtacce sannan haziki a fannin shugabanci.

Taron ya tattaro mata daga jihohin arewa daban-daban da sauran masu ruwa da tsaki da nufin cimma burin buri.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like