Connect with us

Siyasa

Gwamnan Jihar Zamfara Jagora Ne Kuma Mujaddadi – Dokta Suleiman Shu’aibu Shinkafi

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

AN bayyana Gwamnan Jihar Zamfara a matsayin jagora kuma mujaddadin tabbatar da ci gaban kawo alkairi a Jihar da kasa baki daya.

Mai ba Gwamnan Jihar Zamfara Shawara a kan harkokin hulda da yarjejeniya da kasashen waje, Dokta Suleiman Shu’aibu Shinkafi, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da wata tawagar manema labarai a Kaduna.

Dokta Suleiman Shu’aibu Shinkafi, ya ci gaba da cewa hakika Gwamnan Jihar Zamfara Muhammadu Bello Matawalle ya yi rawar ga ni da za a iya bayar da labari ga duniya irin kokarin da ya aiwatar wajen ci gaban Jihar.

Ya ce, “hakika kashin bayan ci gaba da zaman lafiya shi ne a samu sulhu da za a iya yin tafiya tare kai a hade tsakanin jiga- Jigan Jihar Zamfara.

Gwamna Matawalle hakika ya ajiye tarihi gagarumi domin a tarihin Jihar Zamfara ba wani wanda ya jawo mutanen da suka fandare amma ya jawo su a ta fi tare domin Jihar Zamfara da kuma al’ummarta baki daya su samu ci gaba kamar shi.”

“Ya jawo tsofaffin Gwamnoni irinsu Ahmad Sani Yariman Bakura, Mahmuda Aliyu Shinkafi, Abdul’Aziz Yari Abubakar da kuma su Sanata Marafa da sauransu da dama duk domin a ciyar da Jiha gaba wannan babban tarihi ne da kowa ke alfahari da shi sosai.”

Dokta Suleiman Shinkafi da ke ba Gwamnan Jihar Zamfara shawara a kan hulda da yin yarjejeniya da kasashen waje, ya ce a yanzu dai Allah ya amince kowa daga cikin wadannan Jiga- Jigan sun hango ci gaban Jihar Zamfara kuma sun dunkule wuri daya wannan abin alfahari da farin ciki ne matuka.

Dokta Suleiman Shinkafi ya kara da cewa babban dalilin da suka hango ya sa wadannan jiga – Jigan mutane a Jihar Zamfara suka dunkule wuri guda shi ne domin kawai Jihar ta samu ci gaban da ya dace ta samu ne.

“Saboda idan sun zauna a yanayi na baraka ba za a samu ci gaban Jihar Zamfara ba amma a halin yanzu sun dunkule wuri guda kuma jama’a na farin ciki da wannan haduwa ta su domin Talakawa za su samu sauki kwarai”, Inji Dokta Shinkafi.

Ya ce muna nan tare da su mun rungume su za kuma mu ta fi tare har a cimma duk wata nasara a Jihar Zamfara.

Game da masu cewa wai ko jam’iyyar APC ta hango faduwa ne a Jihar Zamfara ya sa suka ba da kai? Sai Dokta Shinkafi ya ce ” kamar dai yadda kowa ya sani ne jam’iyyar APC ba za ta fadi ba a Jihar Zamfara, kasancewar babu wata jam’iyya mai tasiri a Jihar Zamfara da ta wuce APC, ba kuma wani Gwamna mai tasiri a Jihar Zamfara da ya kai Gwamna Matawalle saboda haka maganar faduwa ma ai ba ta taso ba mun dai dubi cewa Allah ne ke yin yadda yaso a lokacin da yaso saboda haka dukkan mu baki daya kasa za mu ta fi bayan mutuwa kowa ya girbi abin da ya shuka.

“A kan haka ne Gwamna Matawalle kancewarsa mutum mai tsoron Allah, lissafi da nazari ya ga cewa mulki na duniya fa ba wani abu ba ne shi ya sa ya ga dacewar a zauna tare da sauran yan uwa ayi tafiya tare domin a ceci talakawan Jihar Zamfara kowa ya samu ci gaba saboda duk fadan da ake yi Talakawa ne ke shan wahala”. Inji shi.

Game da batun girin – girin kuwa sai ya fayyace cewa ” su a nasu matsayin ba girin- girin ba, ta yi mai su a nasu wuri har ruwa ma ta kara domin daman can tuni aka rarraba mukamai, mai girma tsohon Gwamna Abdul’Aziz Yari zai ta fi Sanata kuma tsohon Sanata Kabiru Marafa shi ma zai ta fi Sanata an kuma ba wadanda suke nema da dai wani abu mai kama da hakan an ba su hakuri kuma sun hakura an ba su yan majalisu na tarayya da yan majalisu na Jiha kadan domin shi Gwamna ya dace ya rike yan majalisu na Jiha duk baki daya domin shi zai yi aiki da su.

Don haka ya dace ya rike wadanda ya Sani, saboda haka mu tarigaya ta yi mai har ta batse kuma ina tabbatarwa da jama’a an zauna lafiya domin an raba mukamai tun da dadewa kuma da izinin Allah, haka za a ta fi nan da dan lokaci kadan talakan Zamfara zai ga abin mamaki kwarai”.

Saboda haka duk wanda ka ga ya ce baya son wannan hadewar da aka yi baya son zaman lafiya don akwai wanda ya ce bai amince ba misali dan majalisar tarayya mai wakiltar Shinkafi da Zurmi Bello Hassan ai bai amince da hakan ba domin ya ga cewa zaman sulhun da aka yi bai yi masa ba sai ya koma PDP, kuma komawarsa PDP ba za ta hana mu kayar da shi ba”,.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like