Connect with us

Kungiyoyi

Matakan Matawalle Su Ne Hanyar Kawo Karshen ‘Yan Bindiga A Arewa – Kungiyar Dattawan Arewa

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

WATA kungiyar Dattawa Yan kishin Arewacin Najeriya mai suna “Arewa Elders Initiatives and Interactive Group,” sun yaba da irin matakan da Gwamnan Jihar Zamfara Muhammad Bello Matawalle, ya dauka domin yin maganin masu zagon kasa da suke bayar da bayanai ga yan bindiga, wanda dalilin hakan ke haifar da ci gaba a batun matsala kawo karshen ayyukan yan bindigar daji da sauran miyagun ayyuka na rashin tsaro a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

‘Ya’yan Kungiyar, sun bayyana hakan ne a cikin wata takardar bayani ta bayan kammala taron tattaunawa da suka yi da wasu zababbun yan kungiyoyi masu rajin kare Arewa dake zaman kansu, taron an yi masa taken; ‘ Kalubalen da ke fuskantar Arewa maso Yamma da kuma batutuwan da suke a baya na irin nasarar da ake samu wajen yaki da masu satar jama’a da ayyukan yan bindiga gabanin zaben 2023’.

Shugaban wannan Kungiya ta kasa Masanin Hallayar ‘Dan-Adam Honarabul Alhassan Ado Gwadabe ya bayyana cewa sababbin hanyoyin da Gwamna Bello Matawalle ya dauka a baya da na yanzu a Jihar Zamfara sun hada da kama masu bayar da bayanai ga yan Ta’adda (Informants), rufe dukkan layukan wayoyin Sadarwa, hana sayar da mai da tona asirin masu hada kai da yan bindiga ko masu satar jama’a da suke a cikin al’umma da kuma rushe dukkanin wurarensu, da kuma cire masu sarautar gargajiya da shugabannin al’umma da ake zargi da hada baki ko kuma yin sakaci da aikin tabbatar da samar da zaman lafiya a yankin da suke.

Ya’yan Kungiyar, sun yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari, da shugabannin rundunonin tsaro da Gwamnonin yankin da su samar da wadansu dabarun da za su ci gaba da taimakawa wannan yankin da ake da yan bindiga masu satar mutane da ke addabar Jama’ar yankin baki daya, musamman ma da irin rahotannin da ake samu a halin yanzu na kara bazuwar ayyukan yan Ta’adda da suke kashe Jama’ar da ba su ji ba su gani ba a wasu yankunan Jihohin Kaduna, Neja da Kebbi.

Ya’yan Kungiyar, sun tabbatar da cewa a watanni biyu da suka gabata, Jihohin Neja, Kaduna da Kebbi, sun rasa mutane akalla dari biyu a sakamakon yawan hare-haren ta’addanci da ake samu da ake zargin yan ta’adda ne da suke yin ta’addanci a yankunan Kaduna da Jihar Neja da suke samun goyon bayan sirri daga wasu bata gari a cikin al’umma.

“Babban kalubalen da ake samu a wajen yaki da yan bindiga wadanda a yanzu aka bayyana a matsayin yan Ta’adda shi ne a halin yanzu a canza salon yaki da wadanan miyagun ta yin amfani da irin salon da Gwamnan Jihar Zamfara, Honarabul Muhammad Bello Matawalle ya dauka da ake cewa ‘Gama aiki’ na kama masu bayar da bayanan sirri (Informants) aiki da shugabanin jama’a da kuma hanyoyin siyasa, bayar da dukkan taimakon da masu aikin Sa-kai ke bukata da suka hada da kayan aiki da nuna masu goyon baya ga sauran jami’an tsaro da suke aikin kokarin maganin yan ta’adda.

Sauran mahukunta na kasa suyi koyi da salon da Gwamnatin Jihar Zamfara ta dauka na haifar da samun nasara, domin ana tona asirin masu bayar da bayanai a duk inda maboyarsu take, da kuma samun wadansu hanyoyi na musamman wajen yaki da yan bindiga da nufin magance matsalolin tsaro, wanda hakan ya haifar da samun nasara domin an samu raguwar matsalar ba kamar yadda abin yake a can baya ba, illa a wasu wurare da ake ganin ana yiwa barazana.

Hakika da akwai nasara wanda hakan ya samar da samun yanayin zaman lafiya da har mutane ke samun walwalar gudanar da ayyukansu da kuma tafiya daga nan zuwa can a wuraren da a can baya suka yi kaurin suna na ba mai iya zuwa wajen.

Kuma sakamakon rahotannin da aka samu inda mutane sama da miliyan biyu suka taru a cikin babban birnin Gusau, daga Jihohin Najeriya dabam dabam na tsawon kwanaki uku domin yin harkokin al’amuran addini ba tare da samun wani barazana na rahoton kama wani ko satar wani ko wasu ba; hakika abin ya na karfafa gwiwa kwarai domin ana samun ci gaban zaman lafiya sannu a hankali duk da akan samu wadansu yan matsalolin a wasu wurare nan da can.

Don haka, muke bayanin cewa akwai yuwuwar samun hadin kai, fahimtar Juna, amincewa da samun bayanan sirri a tsakanin dukkan hukumomin tsaro da suke cikin wannan aikin da al’umma da nufin daukar matakan da za su kawo nasara.

Saboda daukar matakin soja kawai ba zai yi maganin wannan matsalar ba ta kashe mutane da bata dukiyar jama’a tare da salwantar rayukansu.

Don haka Kungiyar ta Dattawan Arewa ta bayar da shawara ga Gwamnonin Jihohin Kebbi, Neja,Kaduna, Zamfara, Sakkwato da Katsina da su shirya wani babban taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Gusau domin tattauna muhimman batutuwa baki daya da nufin gano wadannan kalubalen gabanin fara ayyukan siyasar shekarar 2023 mai zuwa.

Haka ma Kungiyar tayi Allah wadai da irin zargin goyon baya da wasu sannanun yan siyasa da manyan yankin Arewa ke nuna wa ga wasu da aka kama ko suke tsare a a hannun Hukuma ana bincikensu. Duk da rashin tsaro da yankin yake ciki, wasu yan siyasa na goyon bayan sakin wani na hannun Dan ta’adda Bello Turji da ake ci gaba da bincikenssa; inda suke goyon bayan ya kai kara kotu don neman a bashi hakkinsa na walwala.

Bayanan da Kungiyar ta samu daga kotu ya tabbatar da cewar wani mai aikin bayar da bayanai ga yan ta’addaya, wanda y kitsa da tabbatar da cewa yana hada baki, ya na goyon bayan yin aikin bayar da bayanai ga yan ta’adda a yankin na bukatar kotu ta wanke laifinsa don samun yanci.

Daga wannan batun na karar da aka kai kotu, ya zamo cewa akwai wadansu da suke ikirarin su manya kasa ne; ko yan boko ne masu ilimi tare da hadin guiwar wasu sannanun yan siyasa da hannu wajen yaduwar kai hare haren da ake yi duk da irin kokarin da Gwamnatocin jihohi da na tarayya ke aikatawa domin samun nasarar da kowa ke bukata wajen yaki da matsalar tsaro da nufin kakkabe yan bindiga da masu aikin ta’addanci da wadanda suke hada baki da su.

Dukiya da rayukan jama’a na kara shiga cikin hadari a kowace rana sakamakon matsalar kai hare hare da ake yi kuma duk da haka ana kokarin kawar da kai ana ta harkokin siyasa kawai ba tare da la’akari da wannan muhimman lamari ba da ke barazanar shafar mu baki daya har ma ya cinye mu.

Haka ma Kungiyar tana shawarta shugabannin gargajiya, shugabannin addini, shugabannin al’umma da su kara matsa kaimi wajen kara fadakar da jama’a da kuma a kodayaushe su taimakawa wadanda aka dorawa alhakin kare rayuka da dukiyar jama’a da muhimman bayanai da za su taimaka wajen cimma nasara.

A halin yanzu da watan Azumin Ramadana ke kara matsowa, muna kara roko da babbar murya ga Gwamnatin tarayya, Jihohi da sauran yan Najeriya da su taimakawa wadanda suka tsinci kansu cikin wannan halin har suka gudu daga gidajensu da garuruwansu musamman wadanda suke a sansanin masu gudun hijira suna neman agaji a sakamakon wannan matsalar ta rashin tsaro a cikin al’umma wanda hakan ya sa suke gudun tsira da rayukansu a yankin.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kungiyoyi

Ƙungiyoyin musulunci sun raba wa marayu 900 abinci kyauta a Katsina (Hotuna)

Published

on

Daga Abbas Bamalli

A wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a gidan marayu na Katsina, sama da marayu 900 ne suka sami farin ciki matuƙa a lokacin da suka samu liyafar cin abincin rana, wanda ƙungiyoyi masu zaman kansu na Musulunci na ƙasa da ƙasa suka yi shirya.

Amir Sultana daga ƙasar Turkiyya tare da haɗin gwiwar Munazzama Da’awa Al-Islam (MADA) daga ƙasar Sudan ne suka shirya taron tare da haɗin gwiwar ofishin uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Raɗɗa.

Shugaban ƙungiyoyi masu zaman kansu, Mufti Ahmed, ya bayyana cewa kimanin marayu 700 a ƙaramar hukumar Katsina da 200 a Jibiya ne suka ci gajiyar wannan kyakkyawan shiri.

Ahmed ya jaddada cewa manufarsu ita ce sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu, da ke nuna irin yadda ƙungiyoyin ke gudanar da ayyukan jin ƙai.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya raba wa iyalai dubu 40 tallafin abinci da kuɗi a Konduga

An samo kuɗaɗe don shirin ne ta hanyar gudumawa daga mawadata da ɗaiɗaikun mutane da suka amince da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Mufti Ahmed ya bayyana cewa, “Ta hanyar tallafin mun gina rijiyoyin burtsatse kusan 36 a wurare daban-daban a jihar.”

Ya ci gaba da cewa, “Yana daga cikin shirinmu na yin amfani da ragowar kuɗaɗen wajen sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu a cikin al’ummarmu.

Wani ɓangare na ayyukanmu shi ne rarraba Alƙur’ani mai girma da kuma bayar da tallafin kuɗi ga marasa galihu.” Baya ga cin abincin rana, ƙungiyoyin sun kuma bayar da gudummawar dalar Amurka 400 ga marayun, wanda hakan ya ƙara haɓaka tasirin ayyukansu na alheri.

Alhaji Isah Muhammad-Musa, kwamishinan ayyuka na musamman, ya yaba da wannan mataki na ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda ya ce hakan ya ƙarawa ƙoƙarin Gwamna Dikko wajen tallafawa marasa galihu da marayu a jihar.

Ya bayyana cewa, uwargidan gwamnan ta shirya yin irin wannan aikin na jin ƙai nan ba da jimawa ba, tare da ƙara azama wajen ɗaukaka masu buƙata a cikin al’umma.

Kalli hotona a nan:

Continue Reading

Kungiyoyi

Za a yi taron ƙasashen Musulmai da na Larabawa a Saudiyya kan yaƙin Gaza

Published

on

Saudiyya ta ce za ta karɓi baƙunci taron ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai don tattauna yaƙin Gaza

Ministan zuba jari na ƙasar Saudiyya ya ce, nan da kwanaki masu zuwa ƙasar za ta karɓi baƙuncin taron koli na ƙasashen Larabawa da ƙasashen Musulmai domin tattaunawa kan yaƙin Isra’ila da Falasɗinu.

“Za mu gani a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, Saudiyya ta ƙira wani taron gaggawa na Larabawa a Riyadh,” in ji ministan zuba jari na Saudiyya Khalid Al-Falih, a taron Bloomberg New Economy Forum a Singapore.

KU KUMA KARANTA: An harba rokoki daga Gaza zuwa Tel Aviv

“A cikin kankanin lokaci, makasudin gabatar da waɗannan tarukan guda uku da sauran tarukan ƙarƙashin jagorancin Saudiyya shi ne a kai ga warware rikicin cikin lumana.”

Kamfanin dillancin labaran Etemad ya rawaito cewa, shugaban ƙasar Iran Ibrahim Raisi zai tafi Saudiyya a ranar Lahadi mai zuwa don halartar taron kolin Ƙungiyar Haɗin kan Ƙasashen Musulmai, wadda ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Iran ya kai tun bayan Tehran da Riyadh suka kawo ƙarshen rashin jituwar da aka shafe tsawon shekaru ana yi ƙarƙashin wata yarjejeniya da China ta kulla a watan Maris.

Continue Reading

Jan hankali

Sun yi wa likita dukan kawo wuƙa saboda ‘yar uwarsu ta rasu a Asibiti

Published

on

A ranar Talata ne wani mutum da ɗansa suka fusata inda suka sauke fishin su akan wani babban likita da ma’aikaciyar jinya a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Idi-Aba, Abeokuta bayan da ‘yar uwansu ya rasu a cibiyar.

Rikicin ya ɓarke ne da misalin ƙarfe 2:00 na safiyar ranar Talata, a sashen bayar da agajin gaggawa na asibitin jim kaɗan bayan wata mara lafiya mai shekaru 53 ta rasu.

Shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Ogun, Dakta Kunle Ashimi yayin da yake zantawa da manema labarai, ya yi Allah wadai da harin da ‘yan uwan mamaciyar suka kai wa biyu daga cikin ma’aikatan jinya,akan mutuwar matar a sakamakon ciwon zuciya.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Ashimi ya ce Dr Pelumi Somorin likitan ne wanda abin ya shafa,yayin da ba a tantance ko waye ma’aikaciyar jinya ba.

Ya bayyana cewa mahaifin da ɗan, sun mari likitan yayin da aka sanar da su mutuwar yar uwar su.

A cewar Ashimi, matar ‘yar shekara 53 da aka kawo asibitin da ciwon zuciya mai tsanani, wanda ita kanta bayan binciken da ta kawo daga cibiyar da aka turo ta, ya nuna cewa,ba za ta ɗauki fiye da kwana ɗaya ba, sai dai wani ikon Allah.

“Watau ta kasance a matakin ƙarshe na gazawar zuciyarta. An bayyana hakan ga ’yan uwan ta, lokacin da aka kawo ta wurin, amma duk da haka mun yi imanin cewa,Allah kan iya yin wani abu, kuma muna jin cewa ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin mun taimaka mata.

“Ya taɓa faruwa a baya cewa, wani mutum da ke cikin irin wannan yanayin ya samu sauki tare da kulawar da ta dace.

“Amma abin takaici, wannan majinyaciyar ta mutu da misalin karfe 2 na safe kuma mijin da ɗan marigayiyar suka faɗa kan likitan da ke kula da mara lafiyar lokacin da aka sanar da labarin rasuwarta.

“Sun mari likitan , daga baya kuma suka hau matar mutanen da ke kusa da su suka yi ta jibgarta.

“Waɗannan mutanen kuma sun ci mutuncin wata ma’aikaciyar jinya” in ji shi.

Shugaban ƙungiyar ya ce an sanar da ‘yan sanda game da lamarin, inda ya ƙara da cewa duk da kasancewar ‘yan sanda a wajen,ɗan ya ci gaba da cin mutuncin su.

“An kira ‘yan sanda kuma DPO na ofishin ‘yan sanda na Kempta ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa wurin.

“Duk da kasancewar ‘yan sanda, ɗan mamacin ,ya afkawa wata ma’aikaciyar jinya kuma duk ƙoƙarin kwantar da hankalinsa da aka yi, ya ci tura.

“A karshe an kai mutanen biyu zuwa ofishin ‘yan sanda na Kemta, inda aka ɗauki bayanansu da na likitan da aka kai wa harin, ma’aikacin jinya da kuma shaidun da ke kewaye.”

Shugaban na NMA, ya gargadi ‘yan Najeriya da su daina cin zarafin ma’aikatan kiwon lafiya, yana mai shan alwashin cewa, duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Mun yanke shawarar cewa wannan zai zama na ƙarshe kuma ba za mu yadda a bamu haƙuri ba, mun yanke shawarar mika ƙarar zuwa kotu kuma gobe za mu kasance a kotu.

“An fara duk wata shari’a kuma za mu kai wannan ƙara kotu.

“Muna so mu yi kira da kuma gargaɗi ga duk waɗanda suke zuwa asibitoci a Ogun cewa ƙungiyar likitocin Najeriya, da sauran abokanta da kowane likita, ba za su amince da kalmar “ayi hakuri” nan ba daga yanzu, daga duk wanda ya zagi wani daga cikin membobinmu.

“Za mu yi iya bakin kokarinmu wajen gurfanar da irin waɗannan mutanen kuma ba za mu amince da rokon kowa ba komai girman mutum.

“Don haka, muna rokon duk wanda yake da hankali ya yi tunanin zai iya roƙon mu daga baya don faranta ran jama’a. Ba laifinmu bane”.

Ashimi ya jaddada cewa, cin zarafin ma’aikatan lafiya ya zama ruwan dare gama duniya, wanda har yanzu ba a warware shi ba duk da kamfen da aka yi na daƙile barazanar.

Ya ce “a duniya baki daya, wannan batu ne da ke ci gaba da gudana kuma an gudanar da yakin akan hana hakan, da dama a duk faɗin duniya na yakar tashe-tashen hankula da cin zarafi da ake yi wa ma’aikatan lafiya.

“Musamman a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya a Abeokuta, jihar Ogun da sauran asibitocin da ke kewayen Jihar Ogun waɗanda ke ƙarkashin ikonmu a matsayin kungiyar likitocin Najeriya.

“Mun gudanar da yaƙi da hani,da irin halayyar nan, da dama a kan wannan taron a baya kuma bayan yawan rokon da muka yi, sai da muka roƙi likitocinmu da su karɓi uzurin waɗanda suke yin abun

“Abubuwa irin wannan ba sa raguwa, a zahiri, wannan yana faruwa sau da yawa a lokuta da dama.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like