Connect with us

Labari

Ma’aikatan Najeriya Na Fuskantar Mawuyacin Hali – Shehu Sani

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

AN bayyana ma’aikatan Najeriya a matsayin wadanda ke cikin wani mawuyacin hali.

Kwamared Sanata Shehu Sani ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi ga manema labarai a filin da aka yi taron bikin ranar ma’aikata ta duniya a Kaduna.

Kwamared Shehu Sani ya ci gaba da bayanin cewa duk da matsalar matsin tattalin arzikin da jama’a ke ciki akwai wani mawuyacin halin da su kansu ma’aikatan kasar ke ciki wato dai wahala Goma da Ashirin kenan.

“Bisa ga lalacewar darajar naira da kuma tsadar kayan masarufi a kasuwa saboda haka ne ma’aikata suka taru a nan su na kokarin jaddadawa Gwamnati cewa lallai a tashi ayi wani abu mai yuwuwa game da halin da ake ciki da kuma halin da Talakawa suke ciki domin in ba a yi wannan gyara ba, to za a iya shiga cikin wani hali a kasa baki daya”.

“Kuma ganin irin yadda halin da tattalin arzikin kasa ke ciki na tabarbarewa, misali hatta wasu daga cikin manoma ba su iya zuwa Gonakinsu saboda halin tsaro, yan makaranta ba su iya zuwa makarantar saboda halin tsaro a halin yanzu an rufe jami’o’in Najeriya tsawon wata da watanni kuma Gwamnati ta kasa cimma bukatun kungiyar malaman Jami’o’i saboda haka a rana irin ta yau dole a tunatar da Gwamnati da ta tashi tsaye wajen yin wani abu kafin lamarin ya lalace baki daya.

Sanata Shehu Sani, ya kuma bayyana kwamared Ayuba Waba a matsayin wani mutum da ya cancanci Yabo da jinjina domin ya jagoranci zanga zanga a Jihar Kaduna saboda an take hakkin ma’aikata da kuma korar wasu daga aiki ga kuma wadanda aka dauka ba a biyansu Albashi don haka a kasa baki daya Ayuba Waba ya fadakar da Gwamnati sosai.

“Idan muna son canza kasar nan ya zama wajibi ya zama dole kowa ne dan Najeriya ya fito ya Sanya idanu a kan wadanda za su shugabanci wannan kasar na biyu kuma dole ne a ci gaba da wayar da kan mutane domin kada su rika yin siyasar amsar Maggi, Suga da Gishiri, idan ba haka ba ranar fita daga halin da ake ciki haka za a ci gaba da daummawa a kan mulki.”

“Idan an duba sosai za a ga cewa yan siyasa sun dawo da yaudararsu da suka saba a baya domin a baya ba su zuwa Suna, biki, saukar karatu, Jana’iza ko Coci ko wani sha’ani na masallaci. Amma a yanzu sun dawo da tsohuwar yaudarar da suka saba yi can baya don haka ya ragewa mutanen su amshi maggi, Suga da Gishiri ku kara Dora wasu kan mulki su ci gaba da taka ku su na ci maku mutunci, amma indai talakan Najeriya na neman mafita sai an nuna ba a son yin zalunci domin bayan mutum ya yi maka zalunci sau daya ko biyu ba komai amma idan an yi na uku akwai ganganci kwarai mutane su ci gaba da amincewa.”

“Kaga zababbe an Sace mutane baka ji maganar shi ba an kashe mutane baka ji maganar shi ba amma a yanzu zabe ya karato sun fara zuwa ana rabawa mutane Shinkafa don haka ayi hattara saboda abin da zai faru nan gaba ya fi na yanzu nesa ba kusa ba”, Inji Kwamared Shehu Sani.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like